Masu Garkuwa Da Mutane
Yayin da ake fama da matsalar tsaro a jihar Benue, majalisar jihar ta bai wa Gwamna Alias Hyacinth awanni 72 da ya yi gaggawar nada hadimi a bangaren tsaro.
Gwamna Umaru Dikko Radda na jihar Katsina ya bukaci bai wa mutane damar siyan bindiga a kasuwa don kare kansu kamar yadda 'yan bindiga ke yi a kasuwanni.
Shugabannin jam'iyyar PDP a jihar Plateau na zargin jami'an sojoji a jihar da sace shugaban jam'iyyar da ke yankin Jos ta Kudu, Mista Dung Tari a yankin.
Masu garkuwa sun yi ajalin wani babban dan kasuwa, Alhaji Samiu Jimoh a shagonsa da ke karamar hukumar Mokwa cikin jihar Neja bayan yi musu tirjiya.
'Yan bindiga sun hallaka mataimakin magatakardar Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke jihar Ebonyi, an kashe Innocent Obi ne a gidansa da ke jihar Imo.
Wasu tsagerun yan bindiga sun kutsa kai gidan ɗan majalisar dokokin jihar Kwara da tsakar dare, sun yi awon gaba da matarsa da kuma 'ya'yansa biyu.
Wani mai garkuwa da mutane, Gaiya Usman da jami'an 'yan sanda su ka kama ya bayyana cewa duka kudin fansa Naira dubu 470 kayan sakawa ya siya da su.
Auwal Abdullahi, wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne ya ce ya gode wa Allah da yan sanda suka kama su. Kakakin yan sandan, Muyiwa Adejobi, ya sanar.
Wasu 'yan bindiga sun kai farmaki kan wata motar bas ta fasinja a jihar Benue inda su ka yi ajalin mutum daya tare da raunata wasu mutane guda biyu a wani sabon hari
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari