Kungiyar Izala
Mun ji cewa Saudi za ta saye Kungiyar Newcastle United a kan fam £350m. Kwanaki dai an ta surutun cewa Sheikh Khaled bin Zayed Al Nehayan zai saye kungiyar ta Newcastle.
Shuwagabannin kungiyar Izalatil bidi’a wa iqamatissunnah ta kai ma mashawarcin tsohon shugaban kasa Jonathan a kar harkokin tsaro, Kanal Sambo Dasuki ziyarar jaje a karkashin jagorancin Sheikh Abdullahi Bala Lau.
Kungiyar addinin musulunci ta Izalatil Bid'ah wa Iqamatis Sunnah dake Najeriya ta yi tir, tare da Allah wadai bisa ihun cin mutunci da cin fuska da yayan kungiyar darikar siyasar Kwankwasiyya suka yi ma Malam Isah Ali Pantami.
Kungiyar Jama'atu Izalitil Bid'ah Wa Ikamatis Sunnah JIBWIS, ta shawarci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya dauka duk wasu matakai mafi dacewa wajen magance tarzomar da 'yan shi'a ke haddasawa a kasar nan.
Kungiyar Izala ta yi kira ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari akan ya dawo da shirin da gwamnatinsa ta dauki aniyar gabatarwa a kafa Rugar Makiyaya, domin inganta rayuwarsu.
A Ranar 7 ga Watan Yuli mu ka ji cewa Mai martaba Sarkin Hadejia ya yabawa Gwamna Badaru na bada gudumuwar fili. Musulmai sun samu kwarin gwiwar gina Makaranta watau Jami’ar JIBWIS da za ayi a Jigawa.
Sheikh Jingir ya bayyana ayyukan masu satar mutane a matsayin zalunci, wanda ya kamata kowa ya hada karfi da karfe wajen yakarsa don ganin an shawo kan lamarin, kamar yadda majiyar Legit.ng ta ruwaito.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito shugaban majalisar Malamai ta kungiyar, Sheikh Sani Yahaya Jingir ne yayi wannan gargadi a garin Jos na jahar Filato a babban taron karama juna sani da kungiyar ta shirya.
Yayin da ake faman wahala, Izala sun tafi kasashen waje inda aka ce Sheikh Bala Lau da Kabir Haruna Gombe sun karbi Naira Miliyan 500 da kuma manya motoci daga wani gwamnan Arewa maso yamma a lokacin da ake yakin neman zaben 2019.
Kungiyar Izala
Samu kari