Za'a bude katafaren Masallacin da hedkwatar Izalah ta gina da fatun Layya a Abuja

Za'a bude katafaren Masallacin da hedkwatar Izalah ta gina da fatun Layya a Abuja

  • Kungiyar Izalah ta kammala ginin sabon Masallaci a unguwar Utako dake birnin tarayya Abuja
  • Kungiyar ta bayyana cewa za'a bude wannan Masallaci ranar Juma'a mai zuwa don fara Sallah ciki
  • Izalah ta ce an gina Masallacin ne da kudin fatun layyan da ake karba hannun jama'a lokacin Sallar Eidul Adha

Abuja - Kungiyar da'awa ta addinin Musulunci, Jama'atu Izalatul Bid'a Wa iqaamatus Sunna JIBWIS za ta bude sabon Masallacin da ta gina a birnin tarayya Abuja ranar Juma'a.

Jibwis a jawabin da ta saki ranar Talata ta bayyana cewa an gina ne da kudaden fatun layya da mutane ke badawa fisabilillah.

Izalah ta bayyana hotunan Masalaccin dake unguwar Utako, kwaryar garin Abuja.

Masallacin da hedkwatar Izalah
Za'a bude katafaren Masallacin da hedkwatar Izalah ta gina da fatun Layya a Abuja Hoto: Jibwis Nigeria
Asali: Facebook

Kara karanta wannan

Dan a mutun siyasa ya mutu yana tsaka da murnar sauya shekar Uban Gidansa daga APC zuwa PDP

Jawabin yace:

"Wannan shine Sabon masallacin da Izala ta gina da kudaden fatun layyan da kuka bada sadaka a unguwar Utako dake tsakiyar birnin Abuja a Naijeriya.
Masallacin angina shi karkashin jagorancin Shugaban IZALA Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau, kuma an masa aiki na musamman wanda za’a jima ana morar sa.
Kuma Ranar Juma’an nan dake tafe za’a bude masallacin domin fara sallah da sauran ayyuka na ibada a ciki insha Allah.
Jin-jina na musamman ga shugaba Sheikh Bala Lau, da sauran shugabanni masu Rufa masa baya. Allah ya saka wa kowa da alheri. Amin."

Kalli hotunan Masallacin:

Masallacin
Za'a bude katafaren Masallacin da hedkwatar Izalah ta gina da fatun Layya a Abuja Hoto: Jibwis Nigeria
Asali: Facebook

Za'a bude katafaren Masallacin da hedkwatar Izalah ta gina da fatun Layya a Abuja
Za'a bude katafaren Masallacin da hedkwatar Izalah ta gina da fatun Layya a Abuja
Asali: Facebook

Za'a bude katafaren Masallacin da hedkwatar Izalah ta gina da fatun Layya a Abuja
Za'a bude katafaren Masallacin da hedkwatar Izalah ta gina da fatun Layya a Abuja
Asali: Facebook

Kungiyar Izala ta rabawa yan gudun Hijra da matsalar tsaro ta shafa a Neja kayayayyki

A wani labarin, kungiyar JIBWIS ta kai dauki ga al'ummar jihar Neja da rikicin rashin tsaro ya kora daga muhallansu.

Kayan da aka raba sun hada da hatsi, tufafi da kayan shayi.

Kara karanta wannan

Diyar tsohon Sarkin Kano Sanusi II da ke Saudi ta bayyana wani mummunan halin Larabawa

Izalah a jawabin da ta saki ta bayyana cewa shugabanninta na reshen Neja sun raba wadannan kayan abinci ne ga yan gudun Hijra daga kananan hukumomin jihar 13.

Kungiyar tace "ta bada wannan tallafi ne ga yan gudun hijira dan rage masu radadin da suke fama dashi na rayuwa sakamakon fitin tinun yan ta'adda da ya raba su da garuruwan su."

Asali: Legit.ng

Online view pixel