Zaben jihohi
Sanatan jam'iyyar Peoples Democratic Party ( PDP) a jihar Ebonyi, Obinna Ogba, ya bayyana cewa PDP ita ta janyowa kanta rashin nasarar da tayi a zaɓen jihar.
Babban faston kasar Primate Elijah Ayodele, ya gargadi Gwamna Dapo Abiodun da wasu zababbun gwamnoni biyu da kada su yi farin ciki tukuna don za a iya tsige su.
Jam'iyyar PDP ta tubure inda ta bayyana cewa lallai sai dai a sauke Mallam Hudu Yunusa Ari daga matsayin kwamishinan zaben jihar Adamawa kafin ran 15 ga Afrilu.
An kalubalanci CBN a kan batun canza kudi, Bello Matawalle ya fito fili ya na cewa sukar canjin takardun kudi da aka yi gabanin zaben bana ya jawo aka doke shi.
Wasu matasa a ƙarƙashin wata ƙungiya, Concerned FCT Youth Group (CFYG) na neman hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) da ta soke zaɓen sanatan birnin tarayya.
Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, na jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ya nemi ƴan adawar jihar da su haƙura su marawa zababben gwamnan jihar baya.
A zaben da aka yi a bana, duk da jam’iyyarsa ta PDP ba tayi nasara a Abia ba, Okezie Ikpeazu ya bada shawarar a hakura da zuwa kotu domin ayi shari’a da LP.
Yayin da zaben jihar Kogi ke karatowa, akwai jerin mutum uku da ya kamata ku sani da ke son maye gurbin gwamnan mai ci da zai sauka nan ba da jimawa ba a jihar.
Hukumar zabe mai zaman kanta ta bayyana yin hayar wasu manyan lauyoyi a kasar nan domin yin aiki wajen tabbatar da sahihancin sakamakon zaben shugaban kasa.
Zaben jihohi
Samu kari