Katsina
Rundunar 'yan sandan jihar Katsina ta yi nasarar fafatawa da 'yan bindiga. 'Yan sandan sun dakile yunkurin yin garkuwa da mutane da miyagun suka yi.
Rahotanni sun ce mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara ya kaddamar da gina masallacin Naira miliyan 350 a mahaifarsa da ke karamar hukumar Danja, jihar Katsina.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kaddamar da hare-hare a wasu kauyukan karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina. Sun kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu.
Rundunar 'yan sandan jihar Katsina ta samu nasarar cafke wani ma'aikacin banki da ake zargin ya saci kudi a asusun wani kwastoma. Ya saci kudin ne ta hanyar ATM.
Yan sanda a Katsina sun kama wani rikakken dan damfara da ke satar ATM yana cire kudin mutane. An kama matashin da ya sace matar aure a jihar Katsina.
Gwamnatin jihar Katsina ta sanya ta yi yarjejeniya da kamfanin Faransa domin farfado da tashar lantarki da Lambar Rimi da ta shafe shekaru 20 ba ta aiki.
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya amince da sabon mafi karancin albashi ga ma'aikata. Gwamna Radda zai rika biyan albashin N70,000.
Gwamnatin tarayya ta lissafa jihohi 25 da za su amfana da lamunin $500m da ta karbo daga bankin Duniya. An ce za a yi amfani da kudin wajen inganta albarkatun ruwa.
Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gana da abokansa da suka yi rayuwar yarinta a firamare da sakandare a Daura. Buhari ya saba ganawa da su.
Katsina
Samu kari