Yaki da ta'addanci a Najeriya
Mayaƙan ƙungiyar ƴan ta'addan Boko Haram sun kai mummunan farmaki a jihar Borno. Ƴan ta'addan sun halaka babban limamin ƙaramar hukumar Kaga da wani ɗan sakai.
Wasu miyagun ƴan bindiga ɗauke da makamai sun kai farmaki a jihar Taraba inda suka yi awon gaba da wani babban faston Katolika da wasu mutum biyu.
Rundunar 'yan sanda reshen jihar Kano ta tabbatar da cewa ɗaya daga cikin manyan 'yan daban da take nema, Abba Barakita, ya miƙa wuya tare da wasu 40.
Tsagerun 'yan bindiga sun yi ajalin rayuka huɗu yayin da suka kai hari karamar hukumar Maru a jihar Zamfara, an ce sun shiga har fadar sarkin Maru, Abubakar Maigari.
Nnamdi Kanu zai tashi da N8bn daga hannun Gwamnatin Tarayya tun da IPOB ta yi galaba a Kotu. Alkali ya ce tsare shi da ake ta yi ya saba doka da tsarin mulki.
Gwamnan Katsina, Malam Dikko Radda, ya ce ko alama ba zai nemi tattauna wa da yan bindigan daji ba, maimakon haka zai yaƙe su da karfin soji sai sun tuba da kansu.
Wasu mahara ɗauke da muggan makamai sun yi ajalin wasu yan gudun hijira da suka baro sansanin zasu je kamun kifi a karamar hukumar Gwer ta yamma a Benue.
Ana da labari wasu hare-hare da aka kai a a Birnin Gwari, an kashe mutane akalla hudu a jihar Kaduna, inda aka kai hare-haren ba su da nisa da sojojin kasa.
Tsagerun 'yan bindiga sun halaka jami'in rundunar mafarauta yayin da suka fita sintiri a kan titin Birnin Gwari, sun kuma kashe direbobin motocin haya biyu.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari