Jihar Edo
Gwamna Monday Okpebholo ya bayyana cikakken goyon bayansa kan ayyana dokar ta ɓaci a jihar Ribas, ya tsame kansa daga matsayar gwamnonin Kudu maso Kudu.
Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo ya sha alwashin ba Bola Tinubu kuri'u a 2027 yayin da ya karɓi shugabannin kananan hukumomi 17 da suka sauya sheka zuwa APC.
Jam'iyyar APC ta zama mai rinjaye a Majalisar Dokokin jihar Edo yayin da ƴan Majalisa huɗu daga PDP da LP suka tattara kayansu suka kƙma cikinta.
Matasan jam'iyyar LP sun yi kira ga masu ruwa da tsaki da a gaggauta dakatar da Sanata Neda Imasuen kan yadda ya tafiyar da batun Sanata Natasha Akpoti.
Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya jaddada cewa babi kowa a kujerun sanatocin Edo ta Tsakiya da Anambra ta Kudu, ta aika saƙo ga INEC.
Sarkin Benin da ke jihar Edo, Oba Ewuare II, ya dakatar da hakimai 67 nan take daga sarautarsu saboda rashin biyayya ga fada da kuma cin amanarta.
Babban limamin Edo, Sheikh Abdulfattah Enabulele ya nuna rashin amincewarsa kan matakin kulle makarantu da wasu gwamnonin Arewa suka dauka saboda azumin Ramadan.
Gwamnatin jihar Edo ta gano wasu gidaje da masu garkuwa da mutane suke boye wadanda suka sace a cikin gari. An rusa gidajen tare da gargadin al'umma.
Rundunar ƴan sanda ta samu nasarar kama mutum 4 da wasu ƴan bindiga suka kai farmaki cocin Katolika a jihar Edo, maharan sun yi garkuwa da limami da ɗalibi.
Jihar Edo
Samu kari