Kasar waje
Kasar Saudiyya ta cika alkawarin da ta dauka a watan Janairu cewa za ta buɗe wasu shagunan kwankwadar barasa a birnin Riyadh domin baki 'yan kasashen waje.
Labarai sun zo cewa an jefo bam, an kashe mutane a lokacin sahur a Gaza. sojojin Israila sun bude wuta inda suka hallaka mutanen Gaza da ke zaune a wani gida.
Ambasada Rawhide Bawa, jakadan kasar Ghana a Najeriya ya rasu yana da shekaru 65 a duniya a birnin tarayya Abuja, an tafi da gawarsa zuwa gida domin jana'iza.
Yayin ake ta kiraye-kirayen bude iyakoki ga Shugaba Tinubu a Najeriya, a karshe shugaban ya saurari koken jama'a ya umarci bude iyakokin Najeriya da Nijar.
Wani dan Najeriya ya taki sa'a bayan da ya tsinci wayoyin iPads guda 500 a wurin aikinsa amma da ya kai rahoto ga manajansa, sai aka ce ya rike su an bashi kyauta.
Azumin Ramadan na farawa daga ketowar alfijir zuwa faɗuwar rana, kuma yana ɗaukar daga sa'o'i 12 zuwa 17, ya danganta da inda mutum ya ke rayuwa a duniya.
Fitaccen Fasto, Elijah Ayodele ya ba Shugaba Bola Tinubu shawara kan yawan tafiye-tafiye zuwa kasashen ketare inda ya ce ya kula da lafiyarsa yafi komai muhimmanci.
Fadar shugaban kasa ta fito ta yi magana kan rahotannin da ke yawo dangane da batun cire takunkumin hana 'yan Najeriya biza da kasar UAE ta yi a baya.
Elon Musk, mai kamfanin X ya yi martani bayan daukewar shafukan Facebook da Instagram inda ya ce su kam shafinsa na tafiya yadda ya kamata ba kamar na Zuckerberg ba.
Kasar waje
Samu kari