Bola Tinubu
Sanatocin Arewa sun yi wani zama. su ka bukaci Bola Tinubu ya maidawa Nijar wutan da aka yanke, a bude filin jirgin sama, sannan Sojojin Nijar su bar mulki a 2025.
Yan fansho a Najeriya sun koka wa shugaban kasa Bola Tinubu kan halin da suka shiga sakamakon cire tallafin man fetur. Sun roki Tinubu ya sanya su a tallafin N25k.
Jam'iyyar Labour Party (LP) ta zargi kotun koli da kasa yanke hukunci a karar da Peter Obi ya daukaka. Jam'iyyar ta bayyana hakan a matsayin abun takaici.
Kafin a iya shirya zabuka masu nagarta, Attahiru Jega ya ce akwai gyare-gyaren da ake bukata, daga ciki ayi wa INEC garambawul sannan a gyara dokar zabe ta kasa.
Ministan harkokin cikin gida, Tunji Ojo a ranar Talalat, 28 ga watan Nuwamba, ya bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Tinubu ya bayar da umarni kan iyakokin Najeriya.
Shugaba Bola Tinubu ya nemi amincewar Majalisar Dattawa don kara karbo bashin dala biliyan 8.69 da kuma yuro miliyan 100 wanda Buhari ya sanya wa hannu a watan Mayu.
Shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya aike da wasiƙa mai kunshi da ranar gabatar da kasafin kuɗin 2024 ga majalisar dattawan Najeriya ranar Talata.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana himmatuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu wurin inganta tattalin arziki cikin watanni 15 kacal.
Fadar Shugaban kasa ta bada sanarwa a yau cewa Bola Tinubu zai kasar waje. Bola Tinubu zai tafi Dubai a kasar UAE ne domin halartar taron COP28 da za ayi.
Bola Tinubu
Samu kari