Majalisar dokokin tarayya
Tsohuwar mamba a majalisar wakilan tarayya, Fatima Binta Bello, ta miƙa takardar fita daga jam'iyyar PDP nan take a ranar Alhamis, 5 ga watan Oktoba, 2023.
Majalisar dattawa ta tabbatar da zabin Balarabe Abbas Lawal (Kaduna), Dr Jamila Bio Ibrahim (Kwara) da Ayodele Olawande (Ondo) a matsayin ministoci.
An shiga cikin rudani a majalisar dattawan Najeriya a lokacin da ake bakin aiki. Wakilin Jihar Kaduna ya fadi ana kokarin tantance sababbin Ministocin kasar.
Honorabul Abdullahi Balarabe Dabai, mamba mai wakiltar Bakori da Ɗanja a majalisar wakilan tarayya ya roƙi a ba mutane damar ɗauƙar makami su kare kansu.
Shugaba majalisar dokokin jihar Ondo ya musanta raɗe-raɗin cewa suna kulle-kulle ta karkashin ƙasa za su tuge matainakin gwamnan jihar, Lucky Aiyedatiwa.
Tsohon gwamnan jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya bukaci gwamnatin jihar da ta dakatar da fansho da sauran alawun dinsa har zuwa sanda zai bar majalisa.
Kamfanin mai na NNPC ya bayyana irin ribar da ya samu a cikin watanni uku na shekarar 2023, ya ce ya samu ribar Naira biliyan 18.4 wanda bai taba samu ba.
Kotun daukaka kara ta rusa nasarar da dan majalisar wakilai, Ndudi Elumelu ya yi na jam'iyyar PDP, kotun ta bai wa Ngozi Okelle ta jamiyyar Labour nasara.
Majalisar wakilai a Najeriya ta dakatar da shirin mika wani yanki na jihar Adamawa ga kasar Kamaru, yankin Sina na karamar hukumar Michika da ke jihar.
Majalisar dokokin tarayya
Samu kari