Tinubu, Fubara Sun Dawo Najeriya ana Shirin Dawo da Gwamnan Ribas Kujerarsa

Tinubu, Fubara Sun Dawo Najeriya ana Shirin Dawo da Gwamnan Ribas Kujerarsa

  • Shugaba Bola Tinubu da dakataccen Gwamna Siminalayi Fubara sun katse tafiyarsu zuwa ƙasashen waje
  • Wannan ya biyo bayan shirin da ake yi na miƙa mulki ga Fubara domin dawo da mulkin dimokiraɗiyya a Ribas
  • Tuni jami'in da ya kula da jihar bayan dakatar da Ɗibar, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas ya fara shirye-shiryen mika mulki

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa. Jihar Rivers – Shugaba Bola Tinubu da gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara, za su koma Najeriya yau Talata.

Matakin ya zo a daidai lokacin da ake shirin kammala mulkin rikon kwarya da Shugaba Tinubu ya kakaba wa jihar a ranar Alhamis.

Fubara zai dawo kujerarsa
Hoton Siminalayi Fubara da Bola Ahmed Tinubu Hoto: Sir Siminalayi Fubara/Bayo Onanuga
Source: Twitter

Sanarwara Hadimin Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga ya wallafa a shafin X ta ce Tinubu, wanda ya tafi hutu zuwa Faransa da Birtaniya tun ranar 4 ga Satumba, ya kammala hutunsa da wuri.

Kara karanta wannan

Atiku ya sake yi wa gwamnatin Tinubu saukale, ya fadi abin da ta gaza magancewa

Bola Tinubu zai komo Najeriya

Jaridar Punch ta ruwaito cewar mashawarcin Shugaban Kasa a kan harkokin labarai, Bayo Onanuga ya ce Tinubu zai koma ofishinsa bayan ya sauka a Abuja.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A lokacin da yake birnin Paris, Tinubu ya gana da Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, a fadar Élysée.

Taron ya tattauna kan dangantaka tsakanin Najeriya da Faransa tare da shirin ƙara haɗin gwiwa a fannoni daban-daban.

Tinubu: Ana shirin mika mulki a Ribas

Yanzu haka, hankula sun karkata kan shirin mika mulki wanda zai kawo ƙarshen mulkin soja na wucin gadi da Tinubu ya sa a jihar.

Vice Admiral Ibok-Ete Ibas, wanda ya shugabanci jihar a lokacin dokar ta-baci, ya fara tsari da bikin godiya a Fatakwal ranar Lahadi.

Haka kuma, an shirya gabatar da lacca ta musamman a Fadar Gwamnati yau Talata, 16 ga Satumba, mai taken “Dimokuraɗiyya da Kyakkyawan Mulki”.

Siminalayi Fubara zai dawo Najeriya a ranar Alhamis
Hoton dakataccen Gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara Hoto: Sir Siminalayi Fubara
Source: Instagram

Ibas ne za a girmama a wajen taron, tare da fitattun baƙi da aka gayyata tun kafin ƙarfe 9:30 na safe.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya yanke hutunsa, ya sanya lokacin dawowa Najeriya

Ana kuma sa ran Fubara, wanda ya dade a Landan, zai dawo yau Talata, bayan jinkirin da ya hana shi dawowa a ranar Litinin.

Wani makusancinsa ya shaida wa jaridar cewa:

“Gwamna zai dawo a ranar Talata kafin a dawo da shi ofis a ranar Alhamis, 18 ga Satumba.

Dawowar Tinubu zuwa Abuja da kuma Fubara zuwa Ribas ya ƙara jawo hankalin ‘yan kasa kan sauyin siyasa da za a samu a ƴan kwanaki masu zuwa.

Fubara zai koma kan mulkin jihar Ribas

A wani labarin, mun wallafa cewa gwamnatin Jihar Rivers ta tabbatar da cewa ta fara shirin dawo da mulkin dimokuraɗiyya bayan watanni tana karkashin dokar ta-baci.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jiha, Farfesa Ibibia Lucky Worika, ya fitar a ranar Asabar, 13 ga Satumba, 2025.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake sa ran Gwamna Siminalayi Fubara da aka dakatar zai dawo kujerarsa a makon nan, bayan shafe watanni a waje.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng