Ministan Tinubu Zai Ƙara Gaba, Ya Tabbatar da Sha'awar Neman Takarar Gwamna

Ministan Tinubu Zai Ƙara Gaba, Ya Tabbatar da Sha'awar Neman Takarar Gwamna

  • Ministan wuta a gwamnatin Bola Tibubu zai nemi takarar gwamna domin bunkasa siyasarsa yayin da zabe ke kwaratowa
  • Bayo Adelabu, ya fara tuntubar jiga-jigan APC a jihar Oyo domin cimma burinsa na tsayawa takarar gwamna a 2027
  • Adelabu ya roki gafara daga mambobin jam’iyya da suka fusata, ya ce ba za a tilasta dan takara ba a zabe mai zuwa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ibadan, Oyo - Siyasar shekarar 2027 na cigaba da daukar zafi tun kafin fara kamfen yan takara.

Ministan Wuta, Bayo Adelabu, a ranar Juma’a ya gana da shugabannin APC da jiga-jigan jam’iyyar a Ogbomoso da Oyo a jihar Oyo.

Ministan Tinubu ya ce zai nemi takarar gwamna
Ministan wuta ya nuna sha'awar neman takarar gwamna a Oyo. Hoto: Adebayo Adelabu.
Asali: Twitter

Ministan Tinubu ya fara shirin takarar gwamna

Yayin da yake jawabi ga mambobin jam’iyyar a Ogbomoso, a gidan wani jagoran jam’iyyar, Ayoade Adeseun, ministan ya ce ya fara saita hanyar siyasarsa, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce wannan ganawar wani bangare ne na tuntuba kan sha'awar tsayawa takarar gwamna a jihar Oyo.

Adelabu ya ce wannan tuntuba na da nufin cimma burinsa na tsayawa takarar gwamna a 2027 a jihar Oyo karkashin jam’iyyar APC.

Yayin da yake neman goyon bayansu, Adelabu ya roki gafara daga wadanda suka fusata, yana mai cewa dole a hada kai don dawowar APC.

Ya ce:

“Na zo in sanar da ku cewa ina son tsayawa takarar gwamnan Oyo a 2027. Zan gwada kwarewata ta baya.
“Ina son in gwada abin da na koya a zabukan baya. Ba na adawa da kowane yanki. Lokacin Allah ne mafi alheri."

- Cewar Adelabu

Adelabu ya kuma bukaci al’ummar yankin su mara wa Bola Tinubu baya don sake lashe wa’adin mulki, domin cigaban yankin da kasa baki daya.

Ya kara da cewa:

“Yanzu ne lokacin Yarabawa su ci gaba da mulkin Najeriya. Idan Tinubu ya dawo, Najeriya za ta ci gaba sosai.”

Ministan Tinubu ya fara tuntuba kan takarar gwamna
Ministan Tinubu ya nuna sha'awar neman takarar gwamna a Oyo. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Twitter

Alkawuran da Adelabu ya dauka a Oyo

A garin Oyo, Adelabu ya nemi goyon baya, yana cewa zai kafa gwamnati mai dauke da kowa da kowa, babu wanda za a bari a gefe, Daily Trust ta ruwaito.

Ya ce:

“Ina son mutane su gane cewa ba za a tilasta wani dan takara ba. Zan yi aiki, in tabbatar da cancanta ta.
“Oyo gida na ne na biyu. Magoya bayana da abokan tafiyata duk suna nan. Suna goyon bayana a baya kuma za su ci gaba.
“Zan ba da hakkin Oyo yadda ya kamata. Oyo yanki ne na tarihi, mai albarka da daraja a fadin jihar.”

An bukaci Tinubu ya kori ministan wuta

Mun ba ku labarin cewa matasa sun buƙaci a kori ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu da shugaban kamfanin rarraba wuta na ƙasa TCN.

Kungiyar matasan NYTGG ta ce akwai sakaci a yawan lalacewar babban layin lantarki wanda ya samu matsala sau uku a mako guda.

A cewar kungiyar, rashin wuta ya jefa ƴan Najeeiya cikin duhu, ƴan kasuwar da ke amfani da lantarki sun tafka asara mai yawa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.