Plateau: Yayin da Ake Watsewa Tinubu, Hadimin Gwamna Ya Ajiye Aiki, Ya Dawo APC

Plateau: Yayin da Ake Watsewa Tinubu, Hadimin Gwamna Ya Ajiye Aiki, Ya Dawo APC

  • Wani a gwamnatin Plateau ya yi murabus daga mukamin mai ba gwamnan jihar, Caleb Mutfwang shawara kan harkokin siyasa
  • Letep Dabang ya ajiye mukaminsa a hukumance ranar 30 ga Yuni, 2025 inda ya tabbatar da komawa jam'iyyar APC
  • Dabang ya bayyana godiyarsa ga damar da aka ba shi ya yi aiki da gwamnati, kuma ya ce yana fatan gwamnati za ta ci gaba da samun nasara

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Jos, Plateau - Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Plateau ya rasa daya daga cikin hadimansa kan harkokin siyasa.

Mai ba gwamnan Jihar Plateau, Caleb Mutfwang shawara kan harkokin siyasa, Letep Dabang ya ajiye aikinsa.

Gwamnan Plateau ya yi rashin hadiminsa zuwa APC
Hadimin Gwamna Caleb Mutfwang ya yi murabus. Hoto: Caleb Mutfwang.
Source: Facebook

Murabus dinsa yana kunshe ne cikin wata wasika da aka rubuta ranar 30 ga Yuni, 2025, wacce aka aika wa shugaban ma’aikatan gwamnan, cewar Punch.

Kara karanta wannan

ADC: Tsohon dan takarar gwamna ya fice daga PDP a jihar Kano

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda APC ta yi rashin jiga-jigai a Abuja

Hakan na zuwa ne bayan jam'iyyar APC ta tafka asarar wasu daga cikin jiga-jiganta yayin da ake maganar hadakar jam'iyyun adawa.

Tsohon Ministan Shari'a, Abubakar Malami SAN ya fice daga jam’iyyar APC, yana cewa Najeriya na cikin mawuyacin hali a yau.

Haka nan tsohon gwamnan Rivers, Rotimi Amaechi shi ma ya tabbatar da ficewarsa daga jam'iyyar da ya rike muƙamin minista.

Malami ya ce matsalolin tsaro da na tattalin arziki sun jefa talakawa cikin wahala, yayin da gwamnati ke fifita siyasa fiye da rayukan jama'a.

Hadimin ya koma APC bayan murabus ya yi murabus
Hadimin Gwamna Caleb Mutfwang ya yi murabus a Plateau. Hoto: Caleb Mutfwang.
Source: Twitter

Hadimin Gwamna ya koma APC bayan murabus

Dabang ya sanar da wakilan gwamnan jihar murabus din a yau Laraba inda ya yi godiya ta musamman kan damar da aka ba shi.

Daga bisani, bayan godiya ga Gwamna Caleb Mutfwang, ya yi masa fatan alheri da samun nasara, cewar rahoton Tribune.

Kara karanta wannan

Ministan Buhari, Malami ya fice daga APC, ya zaɓi sabuwar jam'iyyar haɗaka

Sanarwar ta ce:

“Don Allah a karɓi wannan wasika a matsayin sanarwa ta hukuma kan murabus dina daga matsayin mai ba da shawara kan harkokin siyasa.
“Na yaba da damar da aka ba ni na yin hidima da bayar da gudunmawa ga gwamnati a matsayin mai ba da shawara.
"Na kuma kasance tsohon Darakta Janar na yakin neman zaben shugaban kasa/gwamna na PDP a Jihar Filato.
“Na gode da damar da aka bani, kuma ina fatan gwamnatin za ta ci gaba da samun nasara."

An kuma gano cewa Dabang, wanda tsohon shugaban APC ne a jihar, ya koma jam’iyyar da ta yi shekaru takwas tana mulki kafin 2023.

Shugaban jam’iyyar APC na jihar a yanzu, Rufus Bature, ya tabbatar da cewa:

“Eh, yana tare da mu, ya dawo cikakke, a siyasa, babu abokin gaba na dindindin, sai dai neman muradi su tafi tare.”

An zabi kakakin majalisar jihar Plateau

Mun ba ku labarin cewa kakakin majalisar Plateau, Hon. Gabriel Dewan, ya yi murabus, inda aka zaɓi Nanloong Daniel na APC a matsayin sabon shugaba.

Kara karanta wannan

ADC: Atiku ya fara kokarin jawo jagorori zuwa tafiyar fatattakar APC a 2027

Hakan ya biyo bayan taron sirri da Gwamna Caleb Mutfwang don warware rikicin shugabanci da rashin daidaiton siyasar jihar.

Majiyoyi sun ce an sa ran jagorancin Hon. Daniel zai dawo da zaman lafiya da ci gaba ga majalisar Plateau, tare da haɗin gwiwa tsakanin bangarorin gwamnati.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.