ADC: Hadakar Su Atiku Ta Karyata Zaben Jam'iyyar da za a Taru don Kayar da Tinubu

ADC: Hadakar Su Atiku Ta Karyata Zaben Jam'iyyar da za a Taru don Kayar da Tinubu

  • Hadakar Atiku Abubakar ta nesanta kanta daga rahotannin cewa ta amince da jam’iyyar ADC a matsayin dandalin takararta a zaben 2027
  • Ta bayyana cewa ana ci gaba da laluben jam'iyyar da za a yi amfani da ita wajen tabbatar da APC ba ta koma mulki ba bayan babban zabe mai zuwa
  • Mai magana da yawun hadakar, Salihu Moh. Lukman ya zargi wasu da kokarin tayar da husuma a tsakanin jagororin tafiyar saboda son zuciya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT Abuja – Hadakar siyasa da Atiku Abubakar ke jagoranta ta nesanta kanta daga rahotannin da ke cewa ta zabi jam’iyyar ADC a matsayin dandalin da za ta yi amfani da shi a zaben 2027.

Wani jigo a cikin hadakar, Salihu Moh. Lukman, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis a Abuja, inda ya zargi bata-gari da yada labarin karya.

ATIKU
Hadakar Atiku ta nesanta kanta da zaben ADC gabanin 2027 Hoto: Atiku Abubakar
Asali: Facebook

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa Lukman, tsohon 'dan kwamitin gudanarwa na kasa na APC, ya karyata rahoton da ke cewa an nada shi a matsayin shugaban ofishin hadakar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

‘Ba mu zabi ADC ba,’ Hadakar Atiku

Jaridar Blueprint ta ruwaito cewa Salihu Moh. Lukman ya bukaci jama’a da su yi watsi da rahoton, yana mai cewa karya ce tsagwaronta.

A cewarsa, tattaunawa na ci gaba da gudana tsakanin shugabannin hadakar, kuma sanarwar za ta fito daga jagororinta idan an cimma manufa.

Atiku
Kawancen yan adawa ta ce za ta fadi jam'iyyar da za ta zaba nan gaba Hoto: Atiku Abubakar
Asali: Facebook

Sanarwar ta ce:

"Hankalina ya kai ga rahoton cewa an nada ni shugaban ofishin hadakar Atiku. Jama’a su yi watsi da wannan labari domin ba gaskiya ba ne. Ba a yanke irin wannan hukunci ba."

"Haka zalika, labarin da ke cewa hadakar ta zabi ADC a taron da aka yi a ranar Talata, 20 ga Mayu, 2025, karya ce."

Hadakar Atiku ta soki 'yan adawa

Salihu Moh. Lukman ya zargi wasu ‘yan adawa da kokarin yada jita-jita game da zaben jam’iyyar ADC a matsayin dandalin da hadakar Atiku za ta yi amfani da shi.

Lukman ya ce:

"Abin takaici, wasu masu son kawo rudani suna yada labaran bogi da nufin kawo sabani a tsakanin shugabannin hadakar."
"Muna kira ga jama’a da kafafen yada labarai da su yi watsi da irin wadannan labaran karya da son zuciya."

Atiku da Obi sun magantu kan hadaka

A baya, mun wallafa cewa tsofaffin ‘yan takarar shugaban ƙasa a zaben 2023, Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP, sun karyata cewa sun cimma manufa a kan hadakar adawa.

Wani rahoto da ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta da wasu jaridu ya yi zargin cewa Atiku ya miƙa tayin kujerar mataimaki ga Peter Obi domin a hada kai gabanin zaben 2027.

Atiku, wanda ya musanta batun ya ce a ce duk wata ganawa da ake yi tsakaninsu da sauran jiga-jigan ‘yan adawa na da nufin samar da wata sabuwar kafa mai ƙarfi da za ta ceto Najeriya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.