Babban Dalilin da Ya Sa Sanatan PDP Ya Jefar da Lema, Ya Sauya Sheƙa zuwa APC

Babban Dalilin da Ya Sa Sanatan PDP Ya Jefar da Lema, Ya Sauya Sheƙa zuwa APC

  • Hadimin gwamnan jihar Delta ya yi zargin cewa Sanata Ned Nwoko ya bar PDP zuwa APC ne saboda yana tsoron ba zai samu tikiti ba a 2027
  • A makon da ya shige ne, sanatan mai wakiltar Delta ta Arewa ya sanar da ficewa daga PDP a wata takarda da ya miƙawa shugabanni a gundumarsa
  • Sai dai Fred Oghenesivbe ya ce babu wani rikici da ya kori Nwoko daga jam'iyyar PDP face tsoron ba zai kai labari ba a zaɓe mai zuwa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Delta - Wani hadimi na Gwamna Sheriff Oborevwori, Fred Oghenesivbe, ya faɗi mahangarsa kan sauya sheƙar sanata mai wakiltar Delta ta Arewa, Ned Nwoko daga PDP zuwa APC.

Hadimin mai girma gwamnan ya yi zargin cewa sanata Nwoko ya bar PDP saboda yana tsoron ba zai samu tikitin takara ba a zaɓen 2027.

Kara karanta wannan

Gwamnoni sun kinkimo hanyar tayar da sabuwar rigima a jam'iyyar PDP ta ƙasa

Sanata Nde Nwoko.
Hadimin gwamnan Delta ya ce tsoro ne ya kori Sanata Nwoko daga jam'iyyar PDP Hoto: Nde Nwoko
Asali: Facebook

Kamar yadda Punch ta ruwaito, Ned Nwoko ya fice daga PDP a hukumance ranar Juma'a bayan ya miƙa takardar murabus daga zama mamba a gudumarsa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanata Nwoko ya fice daga PDP

A cikin wasikar da ya rubuta mai dauke da kwanan wata 30 ga Janairu 2025, Nwoko, ya sanar da gundumarsa da ke karamar hukumar Aniocha ta Arewa cewa ya fice daga PDP.

"Na rubuta wannan wasika ne don sanar da ficewa ta daga PDP, jam’iyyar da na kasance cikinta tun lokacin da aka kafata a 1998.
“Dalilin da ya sa na yanke wannan shawara shi ne rarrabuwar kawuna da rikicin cikin gida da ke addabar jam’iyyar. Wannan rikici ya sa na ji da wahala mu iya kawo ci gaban al'umma.
"Duk da cewa na yi ban kwana da PDP, ina tabbatar wa ƴan jam’iyyar da magoya bayana cewa a shirye nake na ba da gudummuwa wajen hadin kai da ci gaban Delta ta Arewa.”

Kara karanta wannan

Bayan ba hammata iska a taron PDP, Sanata ya gaji da lamarinta, ya tuba zuwa APC

- Nde Nwoko.

'Tsoro' ne dalilin ficewar sanatan daga PDP

Sai dai a martanin da ya mayar kan lamarin a ranar Lahadi a Asaba, Oghenesivbe, wanda shi ne Darakta Janar na Hukumar Wayar da Kai da Sadarwa ta Jihar Delta, ya ce:

“Sanata Ned Nwoko ya fice daga jam’iyyar ne saboda yana tsoron cewa ba zai samu tikitin PDP a 2027 ba. Dukkanmu mun san cewa zai fice daga jam’iyyar tun da dadewa.
"Wannan lamari na da alaka da siyasar 2027 da neman tikitin tsayawa takara. Yanzu haka a Delta, Sanata Nwoko ba shi da wata alaka da tsarin PDP, kuma ba ya aiki tare da shugabannin jam’iyyarmu.
"Gwamna Sheriff Oborevwori ne jagoran PDP a jihar Delta, amma Sanata Nwoko ya raba gari da shi. Wanna ya sa yake tsoron cewa ba zai samu tikitin PDP a 2027 ba saboda yadda ya wakilci mutane a matakin kasa.”

Gwamnan Delta na shirin komawa APC?

Kara karanta wannan

"Gwamnatinmu ba za ta raga ba," Abba Gida Gida ya zare takobin yaki da rashawa

A wani labarin, kun ji cewa PDP ta musanta raɗe-raɗin da ake yaɗawa cewa gwamna Sherrif Oborevwori na jihar Delta na shirye-shiryen sauya sheƙa zuwa APC.

PDP ta ce labarin kanzon kurege ne sannan ta bayyana waɗanda suka kirkiro jita-jitar da masu ɗaukar nauyinsu a matsayin waɗanda ba su ƙaunar zaman lafiya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262