Kotun Koli: APC Sun Hango Nasara, 'Shirin' Rantsar da Gawuna Ya Kankama a Kano

Kotun Koli: APC Sun Hango Nasara, 'Shirin' Rantsar da Gawuna Ya Kankama a Kano

  • Magoya bayan jam’iyyar APC za su yi kwalliya iri daya idan za a rantsar da Nasiru Yusuf Gawuna
  • ‘Yan APC sun kwallafa rai a mulkin jihar Kano, su na ganin kotun koli za ta tsige Abba Kabir Yusuf
  • Idan hakan ta faru, an yi dinkin riguna masu tambarin Tinubu wanda ‘yan APC za su a ranar a Kano

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Kano - Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta na kyautata zaton yin nasara kan NNPP a kotun koli a shari’ar zaben gwamnan jihar Kano.

Premium Times ta ce magoya bayan APC na reshen Kano sun fara rabon ankon kayan da za a sa ranar rantsar da Nasiru Yusuf Gawuna.

Kara karanta wannan

Watakila Kotun koli ta yanke hukunci a shari’ar zaben Gwamnan Kano nan da kwana 5

Gawuna
APC na sa ran Nasiru Gawuna ya zama Gwamnan Kano Hoto: @Engr_Alkasimfge/Nasiru Gawuna
Asali: Twitter

Ana addu'a domin Abba ya rasa mulkin Kano

Hakan yana zuwa ne bayan ‘ya ‘yan APC sun yi azumi da salloli da addu’o’i domin su sake samun galaba a kan Alhaji Abba Kabir Yusuf.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahoton ya ce tun a karshen makon jiya mabiya APC su ka fara rabon kayan anko a yankin Fagge a birnin Kano domin shirin rantsuwa.

‘Yan APC sun ci burin cewa Nasir Gawuna zai zama gwamna bayan tsige Abba Gida Gida a kotun koli, inda gwamnan ya daukaka kara.

Ana tunanin cikin makon nan alkalan kotun koli za su raba gardamar shari’ar zaben Kano.

'Yan APC a Kano sun yi dinkin ankon Gawuna

Wani Faisal Ibrahim ya ce ya yi dinkin kayansa kamar sauran ‘yan APC, su na jiran lokacin da za a rantsar da Gawuna ya zama sabon gwamna.

Kara karanta wannan

Bidiyon matashi da aka kama bisa zargin kashe mahaifinsa a Kano bayan caka masa wuka

Faisal Ibrahim yana ganin alkalan kotun koli za su ba lauyoyin jam’iyyar APC gaskiya.

Jagororin APC a Fagge irinsu Ahmad Dangwarzo sun raba wannan anko, sun ce idan dai ba a canza tsarin mulki ba, APC ta karbe mulkin Kano.

..."Abba ya tafi kenan"

Legit ta fahimci akwai wadanda su ka tanadi rigunan GawunaHasArrived G & G da za a ci kwalliya da su idan za a rantsar da sabon gwamna.

A bayan wadannan riguna an rubuta Sashe na 177, ma’ana sashen dokar da kotun daukaka kara tayi amfani da shi wajen tsige Abba a 2023.

Tsige Abba ya haifar da zanga-zanga

Ana da labari kotun korafin zabe da na daukaka kara sun ba Nasir Gawuna nasara a zaben Kano da aka yi a 2023, aka rusa nasarar NNPP mai-ci.

A dalilin hakan ne zanga-zangar lumana su ka barke a wasu wurare a jihar Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng