'Inconclusive': Kotu Ta Ayyana Zaben Gwamnan Zamfara a Matsayin Wanda Bai Kammala Ba, Za a Sake Zabe

'Inconclusive': Kotu Ta Ayyana Zaben Gwamnan Zamfara a Matsayin Wanda Bai Kammala Ba, Za a Sake Zabe

  • Kotun daukaka kara ta yi hukunci kan shari’ar zaben gwamnan jihar Zamfara a yau Alhamis 16 ga watan Nuwamba
  • Kotun ta ayyana zaben a matsayin wada bai kammala ba inda ta bukaci sake zabe a wasu kananan hukumomi uku
  • Legit Hausa ta ji ta bakin wani jigon jam'iyyar APC kan wannan hukunci na kotu a zaben jihar Zamfara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Zamfara – Kotun daukaka kara ta raba gardama kan shari’ar zaben gwamna jihar Zamfara, kamar yadda Channels TV ta tattaro.

Kotun da ke zamanta a Abuja ta ayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba inda ta umarci sake zabe a kananan hukumomi guda uku.

Kara karanta wannan

Bayan tsige gwamnan Kano, Malamin addini ya yi hasashen sakamakon hukuncin zaben Kaduna da Nasarawa

Kotun daukaka kara ta rusa zaben Zamfara, ta ayyana shi wanda bai kammala ba
Kotun daukaka kara ta yi hukunci kan zaben jihar Zamfara. Hoto: Dauda Lawal.
Asali: Facebook

Wane hukunci kotun ta yanke a zaben Zamfara?

Kananan hukumomin da abin ya shafa sun hada da Maradun da Birnin Magaji da kuma karamar hukumar Bukuyun, cewar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotun ta yanke wannan hukunci ne a yau Alhamis 16 ga watan Nuwamba a Abuja inda ta yi fatali da hukuncin karamar kotun a baya.

Har ila yau, kotun ta bayyana cewa kotun sauraran korafe-korafen zabe ta yi kuskure wurin kin yin amfani da shaidun jam’iyyar APC.

Wane hukunci karamar kotu ta yanke?

Gwamna Dauda Lawal na jam'iyyar PDP ya yi nasara a karamar kotun da ta yanke hukunci a kwanakin baya.

Karamin Ministan Tsaro a yanzu, Bello Matawalle wanda ya yi takara a jam'iyyar APC shi ya kalubanci hukuncin karamar kotun a baya.

Kotun ta kuma yi fatali da sakamakon zaben da jam’iyyar APC da kuma hukumar zabe ta INEC su ka bayar a karamar hukumar Maradun.

Kara karanta wannan

Kano: Wane hali ake ciki a birnin bayan kwace kujerar Abba Kabir da kotun daukaka kara ta yi?

Martanin jigon jam'iyar APC kan hukuncin

Legit Hausa ta ji ta bakin wani jigon jam'iyyar APC a jihar Gombe, Honarabul Muhammad Abubakar Auwal Akko.

Akko ya ce wannan hukunci abin a yaba ne inda ya ce hukuncin ya yi daidai da abin da mutanen Zamfara su ka zaba.

A cewarsa:

"Wannan hukunci na kotun daukaka kara a jihar Zamfara abin a yaba ne, an yi hukunci daidai da abin da mutane suka zaba.
"Bangaren shari'a ce kadai ta rage wanda talaka ya ke da sauran kwarin gwiwa a kanta.
"Mu na fatan kotun koli za ta tabbatar da wannan hukunci kamar yadda wannan hukunci ya kasance."

Dauda ya sanya dokar ta baci a harkar ilimi

Kun ji cewa, Gwamna Dauda Lawal Dare ya sanya dokar ta baci a bangaren ilimin jihar.

Dauda ya ce hakan ya zama dole ganin yadda gwamnatin baya ta kashe bangaren har kwano.

Asali: Legit.ng

Online view pixel