Sababbin Shugabannin Kwamitoci 8 Da Mataimakansu Da Aka Zaba a Majalisar Dattawa
- Godswill Akpabio ya sanar da Sanatocin da su ka samu shugabanci na kwamitoci na musamman
- Sababbin Sanatoci irinsu Shehu Buba Umar da Asuquo Ekpenyong sun yi dacen rike kwamiti
- Adeyemi Adaramodu da Sanatan Osun ta tsakiya, Salisu Afolabi sun zama Kakakin Sanatoci
Abuja - A zaman farko da majalisar tarayya tayi a makon nan aka kafa kwamitocin da za su jagoranci ayyukan Sanatoci a majalisar dattawa.
Rahoton da aka samu daga Daily Trust ya bayyana cewa an sanar da shugabannin kwamitoci na musamman da kuma mataimakansu a majalisar.
An raba shugabancin ne tsakanin jam’iyyun APC, PDP da kuma SDP. Hakan ya nuna Sanata Godswill Akpabio zai tafi da ‘yan adawa mulkinsa.

Asali: Facebook
Kamar yadda aka saba, Legit.ng Hausa ta fahimci an bar wa Sanatan Nasarawa, Aliu Wadada Ahmed (SDP) shugabancin kwamitin asusun gwamnati.

Kara karanta wannan
Yanzu-Yanzu: Yaron Tinubu Ya Samu Shirgegen Mukami A Majalisa, Bayan Akpabio Ya Nada Mukamai
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Yadda aka yi rabon kujeru:
1. Harkokin majalisa — Titus Zam (Shugaban kwamiti), Opeyemi Bamidele (Mataimakin shugaban kwamiti)
2. Ayyukan majalisa — Sunday Karimi (Shugaban kwamiti), Williams Eteng Jonah (Mataimakin shugaban kwamiti)
3. Dokoki da korafin jama’a — Okechukwu Ezea (Shugaban kwamiti), Khalid Ibrahim Mustapha (Mataimakin shugaban kwamiti)
4. Asusun gwamnati — Aliu Wadada Ahmed (Shugaban kwamiti), Onyeka Peter (Mataimakin shugaban kwamiti)
5. Tsaron kasa— Shehu Buba Umar (Shugaban kwamiti), Asuquo Ekpenyong (Mataimakin shugaban kwamiti)
6. Bin ka’idar majalisa — Garba Musa Maidoki (Shugaban kwamiti), Ede Dafinone (Mataimakin shugaban kwamiti)
7. Yada labarai — Adeyemi Adaramodu (Shugaban kwamiti), Salisu Shuaibu Afolabi (Mataimakin shugaban kwamiti)
8. Kasafi — Olamilekan Adeola (Shugaban kwamiti), Ali Ndume (Mataimakin shugaban kwamiti)
Tsige Abdullahi Adamu
Rahoto ya zo cewa wasu su na so shugaban APC, Sanata Abdullahi Adamu ya sauka daga kujerarsa a NWC domin kawai a ba Kiristocin kasar nan dama.
Ganin Shugaban kasa (Bola Tinubu) da mataimakinsa (Kashim Shettima) duka musulmai ne, hakan ya jawowa Shugaban jam'iyyar APC na kasa cikas.
Asali: Legit.ng