Sababbin Shugabannin Kwamitoci 8 Da Mataimakansu Da Aka Zaba a Majalisar Dattawa

Sababbin Shugabannin Kwamitoci 8 Da Mataimakansu Da Aka Zaba a Majalisar Dattawa

  • Godswill Akpabio ya sanar da Sanatocin da su ka samu shugabanci na kwamitoci na musamman
  • Sababbin Sanatoci irinsu Shehu Buba Umar da Asuquo Ekpenyong sun yi dacen rike kwamiti
  • Adeyemi Adaramodu da Sanatan Osun ta tsakiya, Salisu Afolabi sun zama Kakakin Sanatoci

Abuja - A zaman farko da majalisar tarayya tayi a makon nan aka kafa kwamitocin da za su jagoranci ayyukan Sanatoci a majalisar dattawa.

Rahoton da aka samu daga Daily Trust ya bayyana cewa an sanar da shugabannin kwamitoci na musamman da kuma mataimakansu a majalisar.

An raba shugabancin ne tsakanin jam’iyyun APC, PDP da kuma SDP. Hakan ya nuna Sanata Godswill Akpabio zai tafi da ‘yan adawa mulkinsa.

Majalisar Dattawa
Sanatoci Majalisar Dattawa Hoto: Nigerian Senate
Asali: Facebook

Kamar yadda aka saba, Legit.ng Hausa ta fahimci an bar wa Sanatan Nasarawa, Aliu Wadada Ahmed (SDP) shugabancin kwamitin asusun gwamnati.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Yaron Tinubu Ya Samu Shirgegen Mukami A Majalisa, Bayan Akpabio Ya Nada Mukamai

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Yadda aka yi rabon kujeru:

1. Harkokin majalisa — Titus Zam (Shugaban kwamiti), Opeyemi Bamidele (Mataimakin shugaban kwamiti)

2. Ayyukan majalisa — Sunday Karimi (Shugaban kwamiti), Williams Eteng Jonah (Mataimakin shugaban kwamiti)

3. Dokoki da korafin jama’a — Okechukwu Ezea (Shugaban kwamiti), Khalid Ibrahim Mustapha (Mataimakin shugaban kwamiti)

4. Asusun gwamnati — Aliu Wadada Ahmed (Shugaban kwamiti), Onyeka Peter (Mataimakin shugaban kwamiti)

5. Tsaron kasa— Shehu Buba Umar (Shugaban kwamiti), Asuquo Ekpenyong (Mataimakin shugaban kwamiti)

6. Bin ka’idar majalisa — Garba Musa Maidoki (Shugaban kwamiti), Ede Dafinone (Mataimakin shugaban kwamiti)

7. Yada labarai — Adeyemi Adaramodu (Shugaban kwamiti), Salisu Shuaibu Afolabi (Mataimakin shugaban kwamiti)

8. Kasafi — Olamilekan Adeola (Shugaban kwamiti), Ali Ndume (Mataimakin shugaban kwamiti)

Tsige Abdullahi Adamu

Rahoto ya zo cewa wasu su na so shugaban APC, Sanata Abdullahi Adamu ya sauka daga kujerarsa a NWC domin kawai a ba Kiristocin kasar nan dama.

Ganin Shugaban kasa (Bola Tinubu) da mataimakinsa (Kashim Shettima) duka musulmai ne, hakan ya jawowa Shugaban jam'iyyar APC na kasa cikas.

Asali: Legit.ng

Online view pixel