‘Yan Takara 6 da ke Hangen Kujerar El-Rufai a APC, PDP, LP, NNPP, ADP da PRP

‘Yan Takara 6 da ke Hangen Kujerar El-Rufai a APC, PDP, LP, NNPP, ADP da PRP

Kaduna -A wannan rahoto, Legit.ng Hausa ta tattaro wadanda suke takarar kujerar Gwamna a jihar Kaduna, kuma ana tunanin daga cikinsu za a samu Gwamnan gobe.

1. Uba Sani

Uba Sani shi ne ‘Dan takaran Gwamnan jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar APC. Sanatan mai shekara 52 zai zo ya zama magajin mutuminsa, Nasir El-Rufai.

Asalinsa mutumin Zariya ne, kuma ya yi digirinsa a bangaren Injiniyanci, daga baya ya yi digirgir a fannin tattalin arziki da PGD a kasuwanci a Kalaba da Abuja.

A 1999 Uba Sani ya zama Hadimi ga Shugaba Olusegun Obasanjo, bayan nan ya yi aiki da Nasir El-Rufai a FCTA a lokacin yana Ministan babban birnin tarayya.

A zaben 2011 ya nemi takarar Sanata amma bai samu tikitin PDP ba. Da El-Rufai ya zama Gwamna sai ya nada shi mai bada shawara a kan harkokin siyasa.

Kara karanta wannan

Kano, Kaduna da Jihohi 10 da Sai Gwamnoni, ‘Yan Takara Sun Yi Da Gaske a Zaben 2023

A karshe Uba Sani ya zama Sanatan Kaduna ta tsakiya bayan ya karbe tikitin Shehu Sani, ya kuma lashe zabe. A 2023 aka tsaida shi a matsayin ‘dan takarar Gwamna.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

2. Rt. Hon. Isa Ashiru Kudan

Hon. Isa Ashiru Kudan yana neman kujerar Gwamnan Kaduna a jam’iyyar PDP. An haifi Sarkin Ban Zazzau ne a 1962, ya yi karatunsa tsakanin Kaduna da Kano.

Isa Ashiru Kudan ya samu Difloma a 1985 a harkar kula da kasuwanci, a 1989 ya yi nasarar samun babbar difloma, yana da shaidar Digirgir daga jami’ar BUK a 2001.

Bayan aiki a Ma’aikatun kudi da na kasuwanci na jihar Kaduna da Hukumar tatsar kudin shiga, Kudan ya rungumi siyasa gadan-gadan da aka dawo farar hula a 1999.

An zabi Isa Ashiru Kudan a matsayin ‘dan majalisar dokoki na jihar Kaduna. A shekarar 2007 ya zama ‘dan majalisar wakilan tarayya, a nan ma ya yi shekaru takwas.

Kara karanta wannan

Katsina: ‘Dan Takaranmu a Zaben 2023 Bai Cancanta Ba – Shugaban Jam’iyyar NNPP

Bayan kafa jam’iyyar APC sai ‘dan siyasar ya bar PDP, ya nemi tikitin zama Gwamna a 2014, daga baya ya koma PDP har ya nemi Gwamna a 2019, bai dace ba.

‘Yan Takara
'Yan takaran Kaduna Hoto: el_uthmaan, Vanguard, HunkuyiSuleiman, punchng.com, hayatu4kaduna
Asali: UGC

3. Jonathan Asake

‘Dan takaran jam’iyyar LP a zaben Gwamnan jihar Kaduna a zaben bana shi ne Jonathan Asake. Tsohon ‘dan majalisar wakilan tarayyar zai gwabza da APC da PDP.

Kamar yadda LP tayi karfi a Kudancin Kaduna, Asake ya fito daga yankin ne, har ya taba rike shugabancin kungiyar SOKAPU kafin ya dawo harkar siyasa a 2022.

4. Suleiman Hunkuyi

Suleiman Othman Hunkuyi mai shekara 63 yana neman kujerar Gwamnan Kaduna a jam’iyyar NNPP. Masu nazarin siyasa su na ganin yana bayan APC da PDP.

Suleiman Othman Hunkuyi ya yi digiri daga jami’ar ABU Zariya a 1986. Bayan ya gama karatu ya shiga siyasa har ya zama shugaban karamar hukumarsa ta Kudan.

Tsakanin 2015 da 2019, Hunkuyi ya wakilci Arewacin Kaduna a majalisar dattawa. ‘Dan siyasar yana cikin Sanatocin da suka bar jam’iyyar APC kafin zaben 2019.

Kara karanta wannan

Buni Vs Sherrif: Takaitaccen Bayani Game Da ‘Yan Takarar Gwamnan Jihar Yobe a Zaben Gobe

Ba wannan ne karon farko da Sanatan ya nemi takarar Gwamna ba, ko a 2019 ya shiga zaben fitar da gwani na PDP, amma ya sha kashi a hannun mutumin yankinsa.

5. Sani Mohammed Sha'aban

Wani mutumin Zariya a cikin ‘yan takaran Gwamna a 2023 shi ne Sani Mohammed Sha'aban. ‘Dan kasuwan yana neman mulkin jihar Kaduna a karkashin ADP.

Kafin sauya-shekarsa zuwa jam’iyyar ADP, Sani Mohammed Sha'aban yana cikin wadanda aka kafa APC da su a Kaduna, ya fi shekaru 20 ana damawa da su a siyasa.

Tsakanin 2003 da 2007, Sha’aban ya wakilci mazabar Zariya a majalisar wakilan tarayya, bayan nan ya nemi takarar kujerar Gwamna a ANPP amma bai yi sa’a ba.

6. Hayatu Lawal Makarfi.

A jam’iyyar PRP Malam Hayatuddeen Lawal Makarfi yake neman Gwamnan jihar Kaduna, ya lashe zaben tsaida gwani da aka shirya a watan Yunin shekarar 2022.

‘Dan auta a cikin manyan ‘yan takaran ya yi karatu a makarantun Therbow, Turaki International da Zamani College, daga nan ya tafi jami’ar ATBU ta Bauchi a 2002.

Kara karanta wannan

El-Rufai Ya Fadi Alfarma 1 Da Yake Nema Wajen Tinubu Saboda Gudumuwar da Ya Bada

‘Dan takaran na PRP ya yi aiki da Ahmadu and Partners Limited zuwa shigarsa siyasa a 2014 har ta kai ya zama Mai ba Gwamna Nasir El-Rufai shawara.

A farkon 2016 aka tura Makarfi zuwa KAPWA, Hukumar da ya zama mataimakin Manajanta. Bayan nan ya yi aiki a madaba'ar Belsha Printing Press da NFIU.

Siyasar jihar Legas

A wani rahoto da muka fitar, an ji labari zargi ya zo cewa ana kulle-kullen kashe ‘Dan takaran Gwamnan jihar Legas a karkashin jam’iyyar hamayya ta LP.

Bode George da ya taba zama mataimakin shugaban jam’iyyar PDP ne yake yada maganar cewa akwai masu shirin hallaka Gbadebo Rhodes-Vivour.

Asali: Legit.ng

Online view pixel