Damammakin da APC, PDP Ke Da Shi a Lagas, Kano Da Wasu Jihohi 3 Mafi Yawan Masu Rijista

Damammakin da APC, PDP Ke Da Shi a Lagas, Kano Da Wasu Jihohi 3 Mafi Yawan Masu Rijista

Jam'iyyun siyasa da yan takararsu suna ta lissafi don bunkasa damammakin da suke da shi a zaben 2023 wanda ake gab da yi.

Manyan jam'iyyun siyasa da yan takararsu sune Bola Tinubu na All Progressives Congress (APC), Atiku Abubakar na Peoples Democratic Party (PDP), Peter Obi na Labour Party, da Rabiu Kwankwaso na NNPP.

Yan takarar shugaban kasa
Damammakin da APC, PDP Ke Da Shi a Lagas, Kano Da Wasu Jihohi 3 Mafi Yawan Masu Rijista Hoto: Atiku Abubakar, Bola Ahmed Tinubu
Asali: Twitter

Halin da ake ciki game da Bola Tinubu, Atiku Abubakar, Peter Obi, PDP, APC

Yan Najeriya da dama musamman matasa sun jajirce don sauya makomar kasar a zabe mai zuwa yayin da suka yi rijista sosai don kada kuri'a a yayin zabe.

Jihohi mafi yawan masu rijista na iya taka rawar gani sosai kan dan takarar da zai zama magajin shugaban kasa Muhammadu Buhari a watan Mayu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

2023: Wasu Masu Son Gaje Buhari Abin Dariya Ne, Gwamnan Arewa Ya Tabo 'Yan Takarar Shugaban Kasa

Saboda haka, an lissafo jerin jihohi biyar da ke da mafi yawan masu rijista da kuma damammakin da wadannan jam'iyyun siyasa da yan takararsu ke da shi.

Manyan jihohi 5 da damammakin da APC, PDP da Labour Party ke da shi a cikinsu

Legas, masu rijistan zabe 7,060,195

Jihar Lagas na da kimanin mutum miliyan 20 kuma Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta ta bayyana cewa fiye da mutum miliyan 7 ne suka yi rijista don kada kuri'a a jihar a zabe mai zuwa.

APC na iya lashe zabe a jihar saboda ganin cewa ta lashe jihar a zabukan 2015 da 2019. Dan takarar shugaban kasar jam'iyyar shine kuma tsohon gwamnan jihar.

Kano, masu rijistan zabe 5,921,370

Jihar ta arewa ita ce ta biyu a yawan masu rijistan zabe a 2023. Fiye da mutum miliyan 5 ne suka yi rijista don zabe a jihar bisa kididdigan hukumar INEC.

Kara karanta wannan

Muna Magana da Su – Atiku Ya Kyankyasa Yiwuwar Haduwa da Kwankwaso ko Obi

Kamar jihar Lagas, ana ganin APC ce za ta lashe jihar itama saboda jam'iyyar ke ta kawo jihar tun 2015 sannan ita ta samar da kuri'u mafi yawa ga shugaba Buhari a zabuka biyu da suka gabata.

Kaduna, masu rijistan zabe 4,335,208

Jihar ce ke bin Kano wajen yawan masu rijista inda take da mutum fiye da miliyan hudu.

Bola Tinubu na APC na iya lashe jihar a zabe mai zuwa kasancewar gwamnan ya sha nuna cewa jam'iyya mai mulki ta fi kowa dama a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu.

Rivers, masu rijistan zabe 3,537,190

Jihar na daya daga cikin jihohi mafi zafi a zabe mai zuwa da masu rijistan zabe miliyan 3.5 sabanin miliyan 3.21 da aka samu a 2019.

Atiku Abubakar na PDP na iya kawo jihar duk da rikicin da ya dabaibaye jam'iyyar wanda ya haddasa gaba tsakaninsa da Gwamna Nyesom Wike.

Kara karanta wannan

An Cafke Wani Tsohon Mai Laifi Dauke Da Bindigu Da Layyu A Taron Kamfen Din APC A Kwara

Katsina, masu rijistan zabe 3,516,719

Katsina ce jiha ta biyar a masu yawan kuri'u a zaben 2023. Yanzu haka, fiye da mutum miliyan 3.5 ne suka yi rijista a zabe mai zuwa.

Duk da matsalolin rashin tsaro a jihar, kasancewar shugaban kasa Buhari dan jihar ya sake ba APC damar kasancewa a saman sauran jam'iyyun siyasa a jihar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel