Kada Ku Kuskura Ku Zabi Shugabannin da Ba Su Cancanta Ba, Shawarin Sarki Sanusi Ga ’Yan Najeriya

Kada Ku Kuskura Ku Zabi Shugabannin da Ba Su Cancanta Ba, Shawarin Sarki Sanusi Ga ’Yan Najeriya

  • Tsohon sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya ba 'yan Najeriya shawari kan wanda ya kamata su zaba a 2023
  • Sanusi ya yi tsokaci game da halin da Najeriya ke ciki, da kuma wuraren da ya kamata a mayar da hankali sosai
  • Ana ci gaba da shirin zaben 2023, 'yan Najeriya da dama na bayyana irin shugabannin da ya kamata a zaba

Jihar Legas - Sarkin Kano na 14, kuma tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) ya ba 'yan Najeriya shawarin irin shugabannin da ya kamata su zaba a zaben 2023 mai zuwa.

Muhammadu Sanu II, ya ce ya kamata 'yan Najeriya natsu su zabi shugabannin da ke da kwarewa ta gudanar da kasa a zabe mai zuwa, kuma su kauda batun kabilanci, TheCable ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Mu ba butulu bane: Tinubu ne zan gaji Buhari a 2023, Insha Allahu, Masari ya bayyana dalilai

Sanusi ya bayyana hakan ne a jiya Laraba 24 ga watan Agusta a jihar Legas taron The August Event 2022 da gidauniyar Moses Adekoyejo Majekodunmi tare da hadin gwiwar Asibitocin Santa Nicholas suka shirya.

'Yan Najeriya su natsu kafin zaben shugaba, inji Sanusi
Kada Ku Kuskura Ku Zabi Shugabannin da Ba Su Cancanta Ba, Shawarin Sarki Sanusi Ga ’Yan Najeriya | Hoto: thecable.ng
Asali: UGC

Sanusi ya bayyana cewa:

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

“Ya kamata a titsiye 'yan siyasa domin su fadi shirinsu kan asibitoci da ilimi da sauran muhimman bangarorin da suke da koma baya a kasar nan.
“Gwamnati dai ta daina mutunta wannan sana’ar kuma babu adadin kudaden da za a kashe a fannin ilimi ta albashi a kasar nan da zai kawo sauyi. Likitoci da malamai ya kamata gansu cikin rayuwa mai kyau da mutuntawa."

Ya kuma bayyana cewa, bangare mafi kyau da zai gyara kowace kasa a duniya shi ne ilimi, inda ya koka da cewa, akwai bukatar martaba ilimi da kiwon lafiya a Najeriya.

Kara karanta wannan

Masoyin Inyamurai ne: Jigon NNPP ya fadi abin da Kwankwaso ya shirya yiwa Inyamurai

Game da tattalin arziki

Da yake magana kan yadda Najeriya ke cikin matsin tattalin arziki, Sanusi ya tuna da yadda Najeriya take a baya da kuma a yanzu, rahoton kafar labarai ta Reuben Abati.

Ya ce:

“A 2016, an ga hauhawar farashin kayayyaki zuwa 18%, lamarin da ya sa farashin komai ya ninka akalla sau biyu duk bayan shekaru hudu. Buhun shinkafa da aka ana sayar dashi Naira 8,000 a 2015, yanzu kuma ya kai N35,000.

Ya kuma tuna yadda a shekarar 2011 aka kai ruwa rana game da tallafin man fetur, inda yace gashi a yanzu gwamnatin Buhari na duba kashe akalla N6.7tr da sunan kudin tallafin mai.

Tsohon Sarkin Kano Sanusi Ya Bukaci Matasa Su Daina Fita Waje, Su Tsaya a Najeriya

A wani labarin, tsohon Sarkin Kano, Muhammad Sanusi na biyu, ya yi kira ga matasan Najeriya da su daina barin kasar nan domin neman dama a kasashen waje, rahoton TheCable.

Kara karanta wannan

Kasuwar Maza Inda Mata Ke Zuwa Sayan Mijin Aure a Kasar Indiiya

Jaridar The Cable ta ruwaito cewa Sanusi ya yi wannan kira ne ga matasan yayin da yake jawabi a ranar Lahadi a wani wasan kwaikwayo mai taken 'A Truth in Time.

Taron wanda ya naqalto rayuwa da gogewar tsohon sarkin, Ahmed Yerima, farfesa ne na fannin wasan kwaikwayo a Jami’ar Redeemer, ya rubuta shi, wanda Duke of Shomolu Productions ya shirya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel