Na lura ana neman yi mani taron dangi ne, Bola Tinubu ya fadi dalilin yi wa Buhari gori

Na lura ana neman yi mani taron dangi ne, Bola Tinubu ya fadi dalilin yi wa Buhari gori

  • Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya shiga Legas a karon farko bayan ya samu takarar shugaban kasa
  • ‘Dan takaran na APC ya wanke kan shi daga babatun da aka ji ya yi wajen neman tikitin jam’iyya
  • A lokacin, Tinubu ya ce a dalilinsa ne Muhammadu Buhari da Dapo Abiodun suka dare kan mulki

Lagos - Asiwaju Bola Ahmed Tinubu wanda yake rike da tutar jam’iyyar APC mai mulki ya yi karin haske a kan babatun da aka ji ya yi kwanakin baya.

Daily Trust ta rahoto Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a ranar Litinin, 20 ga watan Yuni 2022, yana cewa ya yi hakan ne saboda ya lura ana neman yi masa kafa.

Da yake jawabi a fadar Mai martaba Sarkin Legas, Oba Rilwan Akiolu, an ji Tinubu yana bayanin fito da abin da ya birne na tsawon shekaru a cikin zuciyarsa.

Kara karanta wannan

To ka ji: ‘Dan takaran APC ya fadi dalilin janyewa Bola Tinubu takarar shugaban kasa

Kamar yadda ya bayyana a ranar Lahadi, ‘dan takaran na APC ya ce an nemi kai shi bango. Hakan ta sa aka ji ya yi wa shugaban kasa da gwamnan Ogun gori.

Tinubu
Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya shigo Legas Hoto: @Mr_JAGs
Asali: Twitter

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Legas ta samu 'Dan takara

Bola Tinubu yake cewa a tarihin jihar Legas, ba a taba samun wani mutumin jihar da ya zama shugaban kasa ba, sai shi ne yake neman karya wannan tarihi.

Duk da irin gudumuwar da Legas ta ke badawa a tarayya, mafi girman matsayin da jihar ta samu a gwamnatim sama shi ne Alkalin Alkalai na kasa a can baya.

“Na dauki wannan yaki domin kafa tarihi. Yakin neman tikitin jam’iyyar APC ya zo da wahala. A lokacin da na kusa kai bango, sai na komawa addu’a.”
“Sannan kuma na yi aman abin da yake cikin rai na a lokacin da na yi tunanin wasu (a jam’iyyar APC) sun yi mani gayya, an shirya mani taron dangi.”

Kara karanta wannan

Ana kishin-kishin, Tinubu ya nuna wanda yake so ya zama Mataimakinsa a zaben 2023

Na godewa Ubangiji, tun da a karshe nayi nasarar samun takarar shugaban kasan.” - Bola Tinubu.

Aikin da ya ragewa APC

Pulse ta rahoto tsohon gwamnan na Legas yana cewa akwai bukatar a wayar da kan al’umma domin su kada kuri’arsu a zaben shugaban kasa na 2023.

Asiwaju Tinubu ya ce muhimmin abu shi ne a ga yadda mutane za su mallaki katin PVC domin jefa kuri’arsu domin ganin mulki ya fada hannun ‘Dan Legas.

Abokin takarar Tinubu

Abdulazeez Yinka-Oniyangi ya ce yawan kuri’u za a duba wajen fito da abokin takarar Bola Tinubu. A makon jiya ne mu ka fitar maku da wannan rahoto.

Oniyangi ya ce Musulmai ba su da rinjaye a Kudu, don haka dole APC ta dauko Musulmin Arewa ya yi takarar mataimakin shugaban kasa a zaben 2023 mai zuwa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel