2023: Ka goya mun baya da zaran ka shiga Abuja, Tinubu ya roki wani ɗan takarar shugaban kasa

2023: Ka goya mun baya da zaran ka shiga Abuja, Tinubu ya roki wani ɗan takarar shugaban kasa

  • Jagoran APC na ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya roki gwamna Ayade kada ya goya masa baya har sai randa ya shiga Abuja
  • Tinubu, ɗaya daga cikin yan takarar shugaban ƙasa karkashin APC ya ziyarci Ayade ne a kokarinsa na samun tikitin APC
  • Da yake jawabi, gwamna Ben Ayade, ya ce a halin yanzu lokaci ya yi mulkin Najeriya zai koma kudanci

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Cross River - Tsohon gwamnan Legas, Bola Tinubu, wanda ke fatan ya ɗare kujerar Buhari a 2023, ya roki gwamna Ben Ayade na Kuros Riba ya goyi bayan takararsa ta shugaban kasa.

Ayade, wanda na ɗaya daga cikin yan takarar shugaban ƙasa a APC, ya gana da Tinubu ne yayin da jagaban ya kai masa ziyarsa har Kuros Riba ranar Laraba, kamar yadda The Cable ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Yan Najeriya sun waye Atiku ba zai samu kuri'u Miliyan 11m ba, Kwankwaso

Gwamna Ben Ayade da Bola Tinubu.
2023: Ka goya mun baya da zaran ka shiga Abuja, Tinubu ya roki wani ɗan takarar shugaban kasa Hoto: Dr. Abdullahi Umar Ganduje OFR/facebook
Asali: Facebook

Da yake jawabi, tsohon gwamnan Legas ɗin ya yi alkawarin haɓaka tattalin arzikin jihar Kuros Riba da zaran ya zama shugaban Najeriya.

Tinubu ya faɗa wa gwamna Ayade cewa:

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

"Nawa shi ne na baka girma kamar yadda kake ganin girma na, ina rokonka a matsayin babban yaya kuma wanda ya fara ayyana shiga takara, kar ka goyamun baya a yau, amma idan ka je Abuja zaka iya goya mun baya."

A wata sanarwa da Ofishin yaɗa labarai na Tinubu ya fitar, Jagoran jam'iyya mai mulki na ƙasa ya ƙara da cewa:

"Ya zama wajibi mu yi aiki tare ba wai don cigaban tattalin arzikin Kuros Riba da haɗin kan mu kaɗai ba, amma har da ƙasar mu baki ɗaya. Hakan ya rataya a kan mu saboda al'ummar mu na yanzu da jikokin mu na gaba."

Kara karanta wannan

2023: Allah ne ya turo Tinubu ya gyara Najeriya, inji fitaccen malamin addini

Lokaci ya yi da mulki zai koma kudu - Gwamna Ayade

A nashi jawabin, gwamna Ben Ayade ya ce lokaci ya yi da kudu zata fitar da shugaban ƙasa, inda ya ƙara da cewa tsarin karɓa-karɓa na nufin yi wa kowa adalci.

"Tsarin karɓa-karɓa na kunshe a cikin kundin mulkin kasa don tabbatar da daidaito, ba don kabila ko yanki-yanki ba, sai don ba kowa haƙƙinsa. Yanzu lokacin kudu ne a 2023."

A wani labarin kuma Jigon APC ya bayyana sunayen yan takara 5 da zasu iya lallasa Atiku cikin sauki a 2023

Honorabul Farouk Aliyu ya ce akwai yan takarar shugaban ƙasa sama da 5 a APC da zasu iya lallasa Atiku cikin sauki a 2023.

Jigon jam'iyyar APC mai mulki ya ce Atiku ba kanwar lasa bane da zasu saki jiki, zasu yi aiki tukuru don tabbatar da nasara.

Asali: Legit.ng

Online view pixel