Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nemi majalisar dattawan Najeriya ta amince ya sake karbo rancen Dala miliyan 516.3 domin aikin gina titin Sakkawato zuwa Badagry
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nemi majalisar dattawan Najeriya ta amince ya sake karbo rancen Dala miliyan 516.3 domin aikin gina titin Sakkawato zuwa Badagry
A labarin nan, za a ji jihohin Arewa takwas da Sanata Abdul Ningi ke ganin ya kamata a hana ayyukan siyasa gabanin zaben 2027 saboda matsalolin rashin tsaro.
Kungiyoyin kwadagon NLC da TUC za su yi taron gaggawa domin daukan mataki bayan shugaba Bola Tinubu ya yi biris da maganar karin albashi a jiya Talata.
Dan majalisa a jihar Zamfara, , Rilwanu Marafa Na Gambo, ya nemi tallafin gwamna Dauda Lawal Dare kan a gaggauta shawo kan rashin tsaron da ya addabi yankinsa.
Wasu fusatattun mata daga yankin Ipo a Ribas sun shiga zanga-zanga domin nunawa mahukunta bacin ransu na rashin wuta da su ke fama da shi a yankunansu.
Gwamnatin tarayya ta ce babu wani gurbataccen man fetur da ake shigowa da shi Najeriya, wanda hakan ya sabawa ikirarin wani jami’in matatar man Dangote.
Gwamnatin Kano karkashin Abba Kabir Yusuf za ta yi ayyuka na musamman domin inganta kiwon lafiya ciki har da samar da cibiyar kula da masu ciwon sikila.
Tsohon gwamnan babban bankin Najeriya CBN, Mista Godwin Emefiele ya buƙaci babbar kotun tarayya mai zama a Abuna ta sakarmasa fasfo dinsa ya fita waje.
Mutuwar Mai shari’a Adegboye Gbolagunte na babbar kotun jihar Oyo, ta kawo cikas ga ci gaba da shari’a da dama a galibin kotunan jihar a ranar Talata.
Shugaba Bola Tinubu ya bayyana alhininsa game da rasuwar Etop Essien, mataimakin kwanturola mai kula da harkokin kudaden shiga a hukumar kwastam ta Najeriya (NCS).
Wani jigon PDP, Rilwan Olanrewaju ya bayyana jihohin Najeriya da ya kamata ace suna biyan sama da N100,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma'aikata.
Labarai
Samu kari