An Tafka Babban Rashi: Tsohon Sakataren Gwamnati Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

An Tafka Babban Rashi: Tsohon Sakataren Gwamnati Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

  • An shiga jimami a jihar Oyo bayan sanar da rasuwar tsohon Sakataren Gwamnatin jihar wanda ya tayar da hankula
  • Marigayin ya rike mukamin SSG a lokacin mulkin marigayi tsohon Gwamnan Oyo, Abiola Ajimobi, kafin rasuwarsa
  • Iyalansa sun sanar da rasuwarsa, inda suka bayyana shi a matsayin uba, miji, kakansu, dan’uwa kuma suka nemi addu’o’i da goyon baya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ibadan, Oyo - Iyalan tsohon Sakataren Gwamnatin Oyo, Alhaji Abdul Waheed Akintola Olajide sun tabbatar da rasuwarsa a jihar.

Rahotanni sun bayyana cewa Olajide, wanda ya rike mukamin SSG a gwamnatin marigayi tsohon Gwamnan Oyo, Abiola Ajimobi, ya rasu ranar Talata.

Tsohon sakataren gwamnatin Oyo, Abdul Waheed Akintola ya rasu
Taswirar jihar Oyo da aka yi rashin tsohon sakataren gwamnati. Hoto: Legit.
Source: Original

Iyalansa ne suka sanar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa da suka fitar ranar Laraba, inda suka bayyana shi a matsayin ƙaunataccen miji, cewar The Guardian.

Kara karanta wannan

'Ba da yawun Musulmin Najeriya ba': ADC ta soki Malamai kan neman a zabi Tinubu

Sun kuma bayyana marigayin a matsayin uba, kaka, kawu, ɗan’uwa da kuma dan uwa na kusa, tare da gode wa Allah saboda rayuwarsa.

Iyalin sun nemi jama’a da su yi musu addu’a tare da ba su goyon baya yayin da suke jimamin rasuwar mamacin.

An yi rashin tsohon sakataren gwamnatin Oyo
Marigayi tsohon sakataren gwamnatin Oyo, Abdul Waheed Akintola da ya rasu Hoto: Adamimogo FM.
Source: Facebook

An shirya gudanar da sallar jana’izar marigayin da ƙarfe 11:00 na safe ranar Laraba a MAN Centre, Oke Ado, Ibadan.

Ƙarin bayani na tafe...

Tsohon SSG a Kwara ta rasu

A baya, mun ba ku labarin cewa an shiga jimami a jihar Kwara bayan samun labarin rasuwar tsohon sakataren gwamnatin jihar (SSG), Alhaji Saka Abimbola Isau.

Marigayin wanda ya taɓa riƙe muƙamin Antoni Janar kuma kwamishinan shari'a na jihar Kwara, ya rasu bayan ƴar gajeruwar jinya a ranar Asabar, 4 ga Janairun 2026.

Gwamnan Kwara, Alhaji Abdulrahman Abdulrazaq ya aika da saƙon ta'aziyyarsa kan rasuwar marigayin wanda ya taka rawa a fagen siyasar jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.