Kawu Sumaila: 'Yadda Kalaman Sanatan Amurka za Su Iya Raba 'Yan Najeriya'
- Sanatan Kano ta Kudu, Kawu Sumaila ya ce kalaman Sanatan Amurka Ted Cruz na iya tayar da rikicin addini a Najeriya da jefa kasar a cikin tashin hankali
- Sanatan ya kara da cewa matsalar tsaron Najeriya ba ta ta'allaka kan addini kaɗai ba, domin ta shafi kowa ba tare da la'akari da addini ko yankinsa ba
- Kawu Sumaila ya bukaci duniya ta mara wa zaman lafiya da haɗin kai baya maimakon a rika kokarin kalamai ko tunzura rabuwar kai a tsakanin al'umma
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Kano – Sanatan Kano ta Kudu, Suleiman Abdurrahman Kawu Sumaila, ya soki Sanatan Amurka Ted Cruz, yana zarginsa da yaɗa bayanan da ka iya ƙara ruruta rikicin addini a Najeriya.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma'a, 24 ga watan Yuli, 2026, Kawu Sumaila ya ce ƙoƙarin Cruz na neman a sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kira da ake gallazawa kiristoci ya kauce wa ka'ida.

Source: Facebook
Jaridar The Cable ta wallafa cewa Sanatan ya bayyana cewa matsalolin tsaro da Najeriya ke fuskanta sun fi rikitarwa fiye da a jingina su da addini kaɗai.
Ba ruwan ta'addanci da addinin - Kawu Sumaila
A ruwayar jaridar The Nation, Sanata Kawu Sumaila ya ce ta'addanci, fashi da makami, garkuwa da mutane da kuma ayyukan masu tayar da ƙayar baya sun shafi Musulmi da Kiristoci tare da kabilu daban-daban.
A cewarsa, bayyana matsalar tsaro tamkar rikicin addini kawai yana juyar da gaskiyar ga gaskiyar lamarin, yana ƙara rarrabuwar kawuna, tare da iya janyo manufofin ƙasashen waje da ba su dace da abin da ke faruwa a Najeriya ba.

Source: Getty Images
Kawu Sumaila ya tuna cewa gwamnatin Shugaba Donald Trump ta cire Najeriya daga jerin CPC a baya bayan an samu ci gaba da kuma tattaunawar diflomasiyya.
Sai dai ya nuna damuwa cewa har yanzu Ted Cruz na ci gaba da matsa lamba domin a mayar da Najeriya cikin jerin, yana mai cewa hakan ya fi kama da ra'ayi na ɓangare guda fiye da nazari na gaskiya kan halin tsaron ƙasar.
Kawu Sumaila ya kalubalanci kiristoci
Sanatan ya roƙi Kiristoci a Najeriya da sauran sassan duniya su yi nazari sosai kafin su amince da duk wata magana da za ta iya haddasa rarrabuwar addini.
Ya ce masoyan Najeriya na gaskiya ya kamata su tallafa wa zaman lafiya, sulhu, haɗin kan mabambantan addinai, ci gaba mai ɗorewa da kuma mutunta ikon Najeriya.
Sanata Kawu Sumaila ya kuma yabawa jami'an tsaron Najeriya, yana cewa Musulmi da Kiristoci na aiki kafada da kafada wajen yaƙi da 'yan ta'adda, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka.
Sanatan ya ƙara da cewa coci-coci, masallatai, kasuwanni, makarantu da ƙauyuka duk sun fuskanci hare-hare, abin da ke nuna cewa matsalar tsaro ta shafi ƙasa baki ɗaya, ba wata ƙungiyar addini kaɗai ba.
Asali: Legit.ng

