Sakon Uwargidan Tinubu ga Al’ummar Musulmi yayin da Ake Shirin Babbar Salla

Sakon Uwargidan Tinubu ga Al’ummar Musulmi yayin da Ake Shirin Babbar Salla

  • Uwargidan shugaban kasa, Oluremi Tinubu, ta shawarci ‘yan Najeriya su rungumi zaman lafiya da hadin kai yayin bikin sallah
  • Sanata Oluremi Tinubu ta kuma roki jama’a su tallafa wa marasa galihu da masu bukata domin yada kauna, tausayi da sabunta fata a kasa
  • Uwargidan shugaban kasar ta ce bikin salla lokaci ne na tunawa da sadaukarwa, biyayya ga Allah da addu’o’in samun zaman lafiya da ci gaba a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Uwargidan shugaban kasa, Oluremi Tinubu, ta bukaci ‘yan Najeriya su rungumi zaman lafiya tare da rayuwa cikin fahimtar juna a fadin kasa.

A sakonta na bikin babbar salla ga Musulmai a Najeriya da ketare, ta ce karfin Najeriya yana cikin hadin kai da mutunta juna tsakanin jama’a.

Oluremi ta shawarci Musulmiana shirin babbar salla
Uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu. Hoto: Sen. Oluremi Tinubu.
Source: Facebook

Babbar salla: Sahawar da Oluremi ta ba Musulmi

Kara karanta wannan

Dalilin da ya sa Tinubu ya cancanci 'yan Najeriya su kara ba shi dama a zaben 2027

Ta bayyana cewa wajibi ne ‘yan Najeriya su ci gaba da karfafa alakarsu tare da aiki tare domin gina kasa mai zaman lafiya da ci gaba, cewar rahoton The Nation.

Sanata Tinubu ta kuma bukaci jama’a su taimaka wa marasa galihu da masu bukata domin kawo sauki da sabunta fata ga rayuwarsu.

“Kada mu manta da hakikanin ma’anar wannan rana ta hanyar tallafa wa makwabtanmu, musamman marasa karfi da marasa galihu a cikinmu. Wadannan ayyukan alheri da karamci na iya sabunta fata tare da kawo sauki ga mutane da dama.”

- Oluremi Tinubu

A cewarta, ayyukan alheri da tausayi ga makwabta musamman masu rauni na daga cikin muhimman darussan da babbar salla ke koyarwa.

Oluremi ta bukaci hadin kan yan Najeriya
Matar Shugaban kasar Najeriya, Oluremi Tinubu. Hoto: Bayo Onanuga.
Source: Facebook

Muhimmancin babbar salla ga Musulmi

Uwargidan shugaban kasar ta ce bikin babbar salla lokaci ne na tunawa da sadaukarwa, biyayya, imani da nuna kauna ga al’umma baki daya.

Ta bayyana cewa ma’anar bikin ta wuce shagulgula kawai domin yana koyar da sadaukar da kai da mika wuya ga nufin Allah, cewar Punch.

Oluremi ya ce:

“Yayin da muke bikin, ina karfafa wa dukkan ‘yan Najeriya gwiwa su rungumi zaman lafiya tare da rayuwa cikin jituwa da fahimtar juna. Karfinmu a matsayin kasa yana cikin hadin kanmu, mutunta juna da kuma kudurinmu na gina al’umma mai cike da kauna da fahimtar juna.”

Kara karanta wannan

Bikin sallah: Gwamna Zulum ya raba shinkafa mai dauke da hoton Tinubu

Ta kuma bukaci ‘yan Najeriya su ci gaba da yi wa kasa addu’ar samun dorewar zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba mai anfani.

A karshe, ta yi wa Musulmai a Najeriya da sauran sassan duniya fatan gudanar da bikin babbar salla cikin farin ciki da kwanciyar hankali.

'Kalubalen tikitin Musulmi da Musulmi' - Oluremi

Mun ba ku labarin cewa uwargidan Shugaban Kasa, Oluremi Tinubu ta bayyana halin da ta shiga a lokacin da mai gidanta, Bola Tinubu ke neman kujerar mulkin Najeriya.

A cikin wani littafi da ta rubutu, ta bayyana cewa zaɓin takarar shugaban ƙasa da Tinubu ya yi a kan tikitin “Muslim‑Muslim” ya raba kan cocinta.

Oluremi Tinubu ta ce bakin jinin da wannan lamari ya jawo bai hana ta ci gaba da bauta wa Ubangijinta ba, har aka samu nasara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.