Gwamna Ya Yi Fatali da Bukatar Malaman Addini, Ya Ki Kashe Masu Kudin Al’umma

Gwamna Ya Yi Fatali da Bukatar Malaman Addini, Ya Ki Kashe Masu Kudin Al’umma

  • Gwamnan Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya yi fatali da bukatar wasu malamin coci bayan sun nemi a kashe masu kudin al'umma
  • Soludo ya ki amincewa da bukatar malaman na Katolika da suke ce gwamnati ta dauki nauyin yin riguna na musamman
  • Gwamnan ya bayyana cewa ba za a yi amfani da kudaden jama'a don riguna na kungiya ba, amma ya amince da tallafin ziyara zuwa gidajen marayu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Awka, Anambra - Gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya fadawa malaman coci gaskiya game da bukatar da suka nema.

Gwamnan ido da ido ya ki amincewa da bukatar malaman na Katolika cewa gwamnati ta dauki nauyin yin rigunan su.

Gwamna ya ki amincewa da bukatar fastoci
Gwamna Chukwuma Charles Soludo na jihar Anambra. Hoto: Prof. Chukwuma Charles Soludo.
Source: UGC

Ya yi wannan bayani ne a yayin bikin 'All Knights Day' da aka gudanar a St. Patrick’s Cathedral na Awka, inda ya jaddada muhimmancin rayuwa bisa ka’ida, cewar Punch.

Kara karanta wannan

'Yadda 'yan Arewa za su zabi Tinubu a 2027,' Uba Sani ya fito da bayanai

Gwamna ya yi fatali da bukatar fastoci

Soludo ya ce ba za a yi amfani da kudaden jama'a ba wajen yin riguna na kungiya, sai dai ya ba da goyon baya ga ziyara na agaji zuwa gidajen marayu.

Ya ce:

"Ba zan yi amfani da albarkatun jihar ba wajen siyan rigunan kungiya. ku dai ku ci gaba da zama haske da gishiri ta hanyar bin ka’idoji."

Gwamnan ya kuma gargadi su kan rabuwa da nuna bambanci, yana mai cewa su hadu da mutane domin kula da fuskar ɗan adam a cikin al’umma.

Ya yaba wa shugabancin coci wajen karfafa ruhin "al’amarin jama’a" kuma ya jinjina wa diocese bisa tsayuwa kan yakar mummunan al’amura.

Gwamna Soludo ya magantu kan dokar jana'iza

Soludo ya bayyana nasarar dokar Jana'iza ta jihar Anambra, inda ya ce tana rage kayatar da suka wuce da kuma bai wa mutane mutuwar da ta dace.

Gwamnan ya kuma ce yana karfafa kokarin yaki da 'yan fashi na addini da ke zaluntar mutane ta hanyar yada abin da ya kira "ceto ba tare da gicciye ba."

Kara karanta wannan

Gwamna na shirin karambanin murabus ya nemi Sanata a 2027

Ya bayyana cewa an rike wasu mutane da dama, suna bada bayanan da suka bayyana, yana mai jaddada cewa sabon Anambra dole ne ya kasance bisa gaskiya.

Wannan taron ya kunshi mista mai alfarma da aka yi wa jagora daga Bishop na Awka, Rabaran Paulinus Ezeokafor, inda aka yi wa’azi kan aikin Ruhu Mai Tsarki, cewar The Nation.

Fassarar da Sakataren Diocese, Rev. Fr. Evaristus Iheanacho, ya yi ya bayyana cewa zama Knight wata hanya ce ta nazari, duba kai, da adalci bisa ka’idoji.

Gwamna Soludo ya musanta shirin kama malamai

A baya, an ji cewa Gwamnatin Anambra ta yi karin haske kan rade-radin cewa tana shirin kama wasu malaman addinin Kirista a jihar.

Gwamna Charles Soludo ya karyata jita-jitar da ke cewa yana kokarin damke malaman addini, musamman Bishof-Bishof na Katolika.

Kwamishinan yada labarai, Dr. Law Mefor, ya ce labarin karya ne da aka kirkira domin tayar da hankalin jama’a da bata sunan gwamnati.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.