Lamari Ya Baci: Hisbah Ta Cafke Malamin Addini a Zamfara kan Zargin Neman Maza
- Dubun wani malamin addini da ake zargi da neman maza ta cika a jihar Zamfara da ke yankin Arewa maso Yammacin Najeriya
- Hukumar Hisbah ta bayyana cewa ta yi caraf da malamin addinin wanda ake zargi da tura hotunan tsiraicinsa ga wani matashi
- Hisbah ta bayyana cewa malamin addinin ya amsa laifinsa inda ya bayyana cewa ya dade yana tare da wannan mummunar dabi'ar
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Gusau, jihar Zamfara - Hukumar Hisbah ta jihar Zamfara ta samu nasarar damke wani malamin addini.
Hukumar Hisbah ta cafke malamin addinin ne kan zargin neman maza da kuma turawa wani saurayi hotunan tsiraicinsa da bidiyon masu neman maza ta wayar salula.

Source: Facebook
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar Hisbah ta jihar Zamfara, Malam Umar Haruna Tsafe, ya fitar a shafin Facebook a ranar Litinin, 11 ga watan Mayun 2026.
Meyasa Hisbah ta cafke malamin addinin?
Sanarwar wadda jami'in hulda da jama'ar na hukumar Hisbah ya fitar, ta bayyana cewa an cafke malamin addinin ne a birnin Gusau bayan binciken da aka gudanar kan zargin da ake yi masa.
Rahoton ya ce hukumar Hisbah ta bayyana cewa yayin binciken da ta gudanar, malamin addinin ya amsa zargin da ake tuhumarsa da shi.
Malamin addinin ya sanar da hukumar Hisbah cewa ya dade yana aikata irin wannan hali tun lokacin da ya ke karatu a makarantar sakandire da ke GTC Maru.
Hisbah ta yi wa malamin addinin nasiha
Shugaban Hukumar Hisbah ta jihar Zamfara, Sheikh Umar Hassan Gusau, ya yi wa malamin nasiha mai ratsa jiki kan illar abin da yake aikatawa.
Hakazalika, Sheikh Umar Hassan Gusau, ya bayyana cewa bayyana masa sakamakon da addinin Musulunci ya tanada ga mutanen da ke aikata irin wannan laifi.
Shugaban na Hisbah ya kara da cewa a matsayinsa na malamin addini kuma shugaban makarantar Islamiyya, ba zai ci gaba da jagorantar ta ba saboda ka da ya gurbata tarbiyyar dalibai.

Source: Original
Wane mataki aka dauka kan malamin addinin?
Daga bisani, hukumar Hisbah ta dauki matakin mika malamin addinin ga kotun shari’ar Musulunci domin ci gaba da gudanar da bincike da daukar matakin da ya dace a kansa.
Daga karshe, hukumar Hisbah ta sanar da cewa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ci gaba da daukar matakai kan duk mutumin ake zargi da aikata laifuffukan da suka ci karo da koyarwar addini da ka’idojin zamantakewa a jihar.
Hisbah ta cafke ango da amarya a Kano
A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar Hisbah ta jihar Kano ta samu nasarar cafke wasu matasa biyar bisa zargin shirya aure ba bisa ka’ida ba, sannan tare da samun amincewar iyayen amarya ba.
Rahotanni sun nuna cewa an kulla auren ne da sadakin da ya yi kasa da kima, abin da ya sabawa tsarin Musulunci da doka.
Daga cikin wadanda aka kama akwai amarya, ango da wasu mutum uku da suka shiga cikin shirin a matsayin shaidu da wakilai.
Asali: Legit.ng

