"A Yi wa Musulmai Adalci," MURIC Ta Yi Kaca Kaca da Gwamnatin Tinubu kan Fifita Kiritoci
- Kungiyar MURIC ta zargi gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da fifita kiristoci sama da musulmi a wasu ayyukanta
- Shugaban MURIC na kasa, Farfesa Ishaq Akintola ya ce dole gwamnatin tarayya ta yi adalci da daidaito a dukkan al'amurranta
- Akintola ya bayyana aikin gina coci da cibiyar hajjin kiristoci da za a gina a Abuja kan N25bn a matsayin misalin banbancin da ake nuna wa Musulmi
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja – Kungiyar kare hakkin Musulmi (MURIC) ta zargi gwamnatin tarayya da nuna wariya kan aikin gina coci da cibiyar hajjin Kirista da kudinsu ya kai Naira biliyan 25.
Za a gina wannan babbar coci da cibiyar ne a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke babban birnin tarayya Abuja.

Source: Facebook
Daily Trust ta ce a wata sanarwa da shugaban kungiyar MURIC, Farfesa Ishaq Akintola, ya fitar, ya kuma soki gwamnatin kan bayar da Naira biliyan 2 ga wadanda rikici ya shafa a jihar Plateau.
MURIC ta taso Gwamnatin Bola Tinubu
Akintola ya soki tallafin da aka ba wadanda rikici ya shafa a jihar Filato ba tare da ba da irin wannan tallafi ga jihohin Borno, Sokoto, Zamfara, Kebbi da Kwara ba.
“Gwamnatin tarayya da kungiyar CAN sun kaddamar da gina wata babbar coci da cibiyar hajji a filin jirgin sama na Abuja da kudinsu ya kai Naira biliyan 25.
“Ya kamata gwamnati ta bayyana dalilin wannan fifiko take nuna wa kiristoci. Musulman Najeriya sun cancanci a yi musu adalci.
"Ana ta ce-ce-ku-ce a masallatai da kafafen sada zumunta na Musulmi kan wannan lamari.”
- Farfesa Ishaq Akintola.
Kungiyar MURIC ta fadi dalilanta
Akintola ya kuma bayyana damuwa kan yadda aka bai wa jihar Plateau Naira biliyan 2, yayin da sauran jihohin da ke fama da irin wannan rikici ba su samu irin wannan tallafi ba.
Ya tambaya ko wannan adalci ne, yana mai cewa bai dace a nuna bambanci tsakanin al’umma ba.

Kara karanta wannan
Kotu ta amince da bukatar gwamnatin Tinubu a shari'ar mutane 6 da ake zargi da shirin juyin mulki
Ya kuma ambaci wani zargin bayar da Naira biliyan 1.2 ga jihohi 19 na Arewa domin bikin Sallah, yana mai cewa ba a bayyana wanda ya bayar da kudin ba.
“Ta yaya za a bai wa jiha guda Naira biliyan 2, sannan a raba 'Naira biliyan 1.2 ga jihohi 19? Shin hakan daidai ne?”

Source: Twitter
Shawarar da MURIC ta ba gwamnati
Kungiyar MURIC ta bukaci gwamnatin tarayya da ta bayyana lokacin da za ta bai wa Musulmi fili makamancin wannan domin gina babban masallacin kasa, tare da irin tallafin da aka bayar wajen aikin cocin.
Ta jaddada cewa dole ne a yi adalci da daidaito tsakanin Musulmi da Kiristoci a dukkan lamurra na gwamnati, kamar yadda Punch ta ruwaito.
Ana zargin ba a yi wa musulmi adalci a Jos
A wani labarin, kun ji cewa wani malamin Musulunci, Imam Tajuddeen Muhammad Adigun, ya yi kakkausar suka kan yadda ake dorawa musulmi laifi a rikicin jihar Plateau.
Malamin ya ce Musulmi ma suna fuskantar hare-hare da kashe-kashe ba tare da samun adalci ba kamar yadda aka yi a baya.
Malamin ya jaddada cewa Musulunci ba ya goyon bayan kashe-kashe ko zalunci, yana mai cewa addinin ya haramta kisan bayin Allah marasa laifi.
Asali: Legit.ng
