An Fara Hararo Sallar Layya, Sarkin Musulmi Ya Ce a Fita Duba Watan Zulki’ida

An Fara Hararo Sallar Layya, Sarkin Musulmi Ya Ce a Fita Duba Watan Zulki’ida

  • Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi da ke jihar Sokoto ta fitar da sanarwa game da duba jinjirin watan Zulki’ida a ranar Alhamis, 16 ga watan Afrilun 2026
  • Sanarwar ta bukaci dukkan al'ummar Musulmi su fita da yammacin ranar Juma'a, 17 ga watan Afrilun 2026 domin duba watan da sanar da hukumomi
  • Wani masanin taurari a Najeriya, Adamu Ya’u Dan America ya yi karin haske game da yadda watan zai fito da batun ganin shi ko akasin haka a Saudiyya

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Sokoto - A jiya Alhamis 16 ga watan Afrilu, 2026, mai alfarma Sarkin Musulmi ya fitar da sanarwa game da fita duba watan 11 a kalandar Musulunci, wato Zulki’ida.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da watan Shawwal ke bankwana, inda ya cika kwana 29 a yau Juma'a 17 ga watan Afrilun 2026.

Kara karanta wannan

'Kano, Yobe': An saki sunayen jihohi 33 da za su fuskanci ambaliyar ruwa a 2026

Sarkin Musulmi yana bayani a wani waje
Sarkin Musulmi yayin wani jawabi ga al'umma a Najeriya. Hoto: Getty Images|Sultanate Council Media Team
Source: Facebook

Legit ta tattaro bayanan da fadar Sarkin Musulmi ta fitar a Facebook a wata takarda da Wazirin Sokoto, Farfesa Sambo Wali Junaidu ya sanyawa hannu.

Za a fita duba watan Zulki’ida

Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi ta bukaci al'umma su fita duba watan Zulki’ida a yau Juma'a tare da bukatar su sanar da hukumomi.

Sanarwar da ta fitar ta ce:

"Ana sanar da daukacin al’ummar Musulmi cewa ranar Juma’a, 17 ga Afrilu, 2026, wadda ta yi daidai da ranar 29 ga watan Shawwal 1447AH, ita ce ranar da za a fara duban jinjirin watan Zulki’ida 1447AH."
"Don haka ana rokon Musulmi da su fara duban jinjirin watan Zulki’ida 1447AH a ranar Juma’a, sannan su kai rahoton ganin jinjirin ga hakimi ko shugaban kauyensu mafi kusa, domin a mika ga mai alfarma, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar."
"Allah (SWT) Ya taimake mu wajen sauke wannan nauyi na addini, amin."

Kara karanta wannan

Gwamnatin tarayya ta fayyace gaskiya game da 'kisan fararen hula' a Borno

Batun ganin wata a Saudiyya a yau

Bayan sanarwar Sarkin Musulmi, masani mai sharhi kan abubuwan da suka shafi taurari, Adamu Ya'u Dan America ya wallafa a Facebook cewa a yau za a ga wata a Saudiyya.

Ya ce:

"Ranar Juma’a 17/04/2026, bayan sallar Magariba, za a samu labarin cewa kasar Saudiyya ta kunna koren haske a saman agogon Ka’aba, wanda hakan ke nuna cewa an ga watan Zulki’ida 1447AH.
"Hakan zai faru ne saboda a ranar Juma’a da misalin karfe 2:51 na rana agogon Saudiyya za a samu haduwar wata da duniya da rana, wanda shi ne asalin samuwar jinjirin wata.
"Haske zai fara bayyana a jikin jinjirin bayan faduwar rana a kasar Saudiyya."
Adamu Ya'u Dan America
Adamu Ya'u Dan America yayin sharhi kan duba wata. Hoto: Adamu Ya'u Dan America
Source: Facebook

Ya kara da cewa Wannan na nufin cewa ranar Asabar 18/04/2026 za ta kasance ranar 1 ga watan Dhul-Qa’ada 1447AH a kasar Saudiyya bisa hasashen da ya yi.

Malami ya sabawa sanarwar Sarkin Musulmi

A wani labarin, mun kawo muku cewa wani malami a jihar Sokoto, Sheikh Musa Ayuba Lukuwa ya sabawa umarnin Sarkin Musulmi yayin sallar azumi.

Kara karanta wannan

An kama ɗan shekara 15 da ake zargi da hannu a kashe Janar a harin Borno

Malamin ya fita sallar Idi tare da mutanensa a Sokoto duk da cewa fadar Sarkin Musulmi ta sanar da cewa za a yi azumi 30 saboda rashin ganin wata.

Cikin dalilan da ya kawo, Sheikh Lukuwa ya sanar da cewa sun samu labarin ganin wata a kasar Nijar saboda haka wannan ya wadatar da su.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng