Amsoshin Tambayoyi 7 kan Harajin Fetur na 5% da za a Kawo a Najeriya

Amsoshin Tambayoyi 7 kan Harajin Fetur na 5% da za a Kawo a Najeriya

Mun tattaro muku amsoshin tambayoyi 7 game da harajin 5% da ake sa ran zai fara aiki a kan man fetur a nan gaba.

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja -'Yan Najeriya na cigaba da tambayoyi game da harajin 5% da ake cewa gwamnatin tarayya za ta fara karba.

Yayin da aka rika musayar yawu kan harajin, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ba a yanke matsaya kan lokacin fara karbar harajin ba.

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu. Hoto: Bayo Onanuga|Getty Images
Source: UGC

A wannan rahoton, mun tattaro muku jerin tambayoyi da amsoshinsu game da dokar da ke cigaba da jan hankalin 'yan Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Tinubu ne ya kawo harajin 5%?

Shugaban kwamitin shugaban kasa a kan gyaran haraji, Taiwo Oyedele ya wallafa a Facebook cewa harajin ba sabon abu ba ne a Najeriya.

Kara karanta wannan

An zo wajen: Gwamnatin Tinubu ta yi magana kan lokacin fara biyan harajin fetur

Ya bayyana cewa yana cikin dokar FERMA ta 2007, saboda haka baya daga cikin sababbin dokokin haraji da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya kawo.

Shugaban kwamitin shugaban kasa kan harkokin haraji. Hoto: Taiwo Oyedele
Shugaban kwamitin shugaban kasa kan harkokin haraji. Hoto: Taiwo Oyedele
Source: Twitter

2. Za a fara biyan harajin a 2026?

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa harajin ba zai fara aiki kai tsaye tare da sababbin dokokin haraji ba.

Sai dai a cewar gwamnatin, ministan kuɗi zai fitar da sanarwar a kan lokacin fara karbar harajin bayan la’akari da yanayin tattalin arziƙi da lokacin da ya dace.

Ministan kudin Najeriya yayin da ya halarci wani taro
Ministan kudin Najeriya yayin da ya halarci wani taro. Hoto: Wale Edun
Source: Getty Images

3. Harajin zai shafi dukkan makamashi?

An ware wasu kayan makamashi da ake amfani da su a gida da ba za su shiga karkashin dokar harajin ba.

Oyedele ya bayyana cewa makamashin da aka ware sun haɗa da man girki na kalanzir, iskar gas ta girki (LPG), da kuma iskar gas ta CNG.

Motoci masu aiki da makamshin CNG da gwamnatin Najeriya ta sayo
Motoci masu aiki da makamashin CNG da gwamnatin Najeriya ta sayo. Hoto: Bayo Onanuga
Source: UGC

4. Me yasa ba a soke harajin 5% ba?

Punch ta wallafa cewa gwamnatin ta ce an yi karin ne a matsayin kuɗi na musamman da za a tara domin gyaran hanyoyi da gina sababbbi.

A cewar gwamnatin tarayya, idan aka yi amfani da kudin yadda ya kamata, zai taimaka wajen rage haɗura a hanya, sauƙaƙa tafiye-tafiye, rage kuɗin sufuri da gyaran mota.

Kara karanta wannan

Yadda za ka lissafa harajin da za ka biya gwargwadon kuɗin da kake samu a Najeriya

Shugaban Najeriya yana sanya hannu a kan wata takarda
Shugaban Najeriya yana sanya hannu a kan wata takarda. Hoto: Bayo Onanuga
Source: Facebook

5. Ina aka kai kudin tallafin mai?

Duk da cewa kuɗin cire tallafin mai zai taimaka wa kasa, gwamnatin tarayya ta ce ba zai isa ya biya buƙatun gina hanyoyi masu yawan gaske a Najeriya ba.

Daily Trust ta rahoto cewa gwamnatin ta ce za a tara kuɗin harajin 5% ne domin tabbatar da an samu tushe mai dorewa da tabbataccen kuɗin yin hanyoyi, baya ga kasafin kuɗi.

Wasu ma'aikata na aikin gina titi
Wasu ma'aikata na aikin gina titi. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

6. Harajin 5% zai kara nauyi ga jama'a?

Gwamnatin tarayya ta ce sauye-sauyen da aka yi sun riga sun rage nauyin haraji da dama kuma sun soke wasu ƙarin kuɗi da suka shafi jama’a da ƙananan masana’antu kai tsaye.

Ta ce harajin 5% ba zai zama karin nauyi ba saboda an cire harajin VAT kan man fetur da harajin tsaron yanar gizo.

Mutane ne na layin sayen man fetur a Najeriya
Mutane ne na layin sayen man fetur a Najeriya. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

7. Za a cire harajin daga dokar FERMA?

Fadar shugaban kasa ta ce an riga an cire shi daga dokar FERMA an haɗa shi cikin sababbin dokokin haraji da aka tsara.

Kara karanta wannan

Wike ya laftawa Ganduje da wasu manya tarar miliyoyin Naira a kan filaye

Gwamnatin ta ce harajin 5% ya tabbatar da cewa Najeriya ta shirya wajen fuskantar manyan ƙalubale, irin su samar da kuɗin hanyoyi a fadin Najeriya.

Mutane ne na layin sayen man fetur a Najeriya
Mutane ne na layin sayen man fetur a Najeriya. Hoto: Getty Images
Source: UGC

Harajin gwamnatin Tinubu zai shafi jama'a

A wani rahoton, kun ji cewa masana sun fara bahasi kan yadda dokar harajin shugaba Bola Tinubu za ta shafi al'umma.

An bayyana cewa dokar za ta shafi kusan dukkan harkokin 'yan Najeriya da zarar ta fara aiki a nan gaba.

Wani bincike ya nuna cewa zai shafi masu sana'o'in hannu da ma'aikatan gwamnati musamman wajen zirga zirga.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng