Malamin Addini Ya Rikita Al'umma da ya Kashe Yara 4 Ƴan Gida Ɗaya da Taɓarya

Malamin Addini Ya Rikita Al'umma da ya Kashe Yara 4 Ƴan Gida Ɗaya da Taɓarya

  • Wani fasto a Ibagwa-Aka, Igbo-Eze ta Kudu, Enugu, ya halaka yara hudu da tabarya lamarin ya girgiza al’umma tare da tayar da hankula
  • Shugaban karamar hukumar, Ferdinand Ukwueze, ya ziyarci iyalan mamatan, ya ce gwamnati za ta tabbatar da an hukunta wadanda ke da hannu
  • Iyayen yaran sun nemi a yi bincike sosai bayan kama wasu da ake zargi, yayin da ‘yan sanda ke ci gaba da farautar sauran da suka tsere

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Enugu - An shiga wani irin yanayi a jihar Enugu bayan wani Fasto ya yi aika-aika na kisan kai wurin amfani da tabarya.

A cikin garin Ibagwa-Aka da ke karamar hukumar Igbo-Eze ta Kudu a Enugu, mummunan lamarin ya girgiza iyali da daukacin al’umma.

Fasto ya hallaka wasu yara
Fasto ya yi ajalin yara 4 a Enugu. Hoto: Legit.
Asali: Original

Fasto ya hallaka yara 4 a Enugu

Faston ya hallaka yara hudu ‘yan uwan juna, Kamsiyochukwu Ezema (7), Ezinne Ezema (6), Ujunwa Ezema (5), da Chinedu Ezema (2) aka kashe da tabarya, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Faston da ke cocin sabbath a yankin ne ake zargin ya aikata wannan kisan, kuma har yanzu ba a san dalilin hakan ba.

Shugaban karamar hukumar Igbo-Eze ta Kudu, Mista Ferdinand Ukwueze, ya nuna bakin ciki da fushi, ya ce dole a hukunta shi idan aka gama bincike.

Ya ce:

“Al’ummarmu ta girgiza da kisan gilla da aka yi wa yaran nan guda hudu a Ibagwa-Aka."

Ukwueze ya kai ziyara wajen da abin ya faru tare da ‘yan sanda, DSS da jami’an tsaro domin duba lamarin da daukar matakin gaggawa.

“Binciken farko ya sa aka kama wasu masu hannu a kisan yayin da aka ci gaba da neman wasu da ke gudun hijira."

- A cewar Ukwueze

Ana zargin Fasto da hallaka yara 4
Hankula sun tashi da Fasto ya kashe yara 4 a Enugu. Hoto: Nigeria Police Force.
Asali: Facebook

Hukumomi sun yi alkawarin hukunta Fasto

Ukwueze ya ba da umarnin a kulle wajen da aka aikata kisan, wanda ake amfani da shi don maganin gargajiya da ayyukan tsafi.

Ya kara da cewa:

“Za mu ci gaba da tallafa wa bincike har sai an hukunta wadanda ke da hannu."

Iyayen yaran, Chinonso Ezema da Loveth Ezema, sun nemi a yi adalci.

Mahaifin ya ce:

“Muna so ‘yan sanda su bincika sosai kuma a hukunta kowa."

Yayin da al’umma ke jimamin rasuwar yaran, hukumomi na kokarin ganin an hukunta masu laifi tare da kare afkuwar irin haka a gaba.

Ana kokarin tuntubar jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar Enugu, SP Daniel Ndukwe, amma bai amsa kiran waya da sakon tes ba.

Matashi ya kashe mahaifiyarsa da tabarya

Mun ba ku labarin cewa ana zargin wani matashi, Safiyanu Dalhatu ya hallaka mahaifiyarsa da tabarya a Bauchi, lamarin da ya jefa al’umma a firgici da jimami.

Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da kama wanda ake zargi tare da kwace tabaryar da ya yi amfani da ita wajen aikata wannan aika-aika.

Binciken farko na 'yan sandan ya nuna rikici tsakanin Safiyanu da mahaifiyarsa ne ya harzuka matashin har ya farmaki gyatumarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.