Shugaba Tinubu Ya Kafa Sabuwar Makarantar Kimiyya da Fasaha, Ya Raɗa Mata Sunansa

Shugaba Tinubu Ya Kafa Sabuwar Makarantar Kimiyya da Fasaha, Ya Raɗa Mata Sunansa

  • Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabuwar kwalejin kimiyya da fasaha a Gwarinpa, ɗaya daga cikin manyan unguwanni a Abuja
  • Rahotanni sun nuna cewa za a raɗawa sabuwar makaranta sunan Bola Tinubu domin girmamama mai girma shugaban ƙasa
  • Shugaban ƙaramar hukumar kwaryar birni watau AMAC ya yabawa Shugaba Tinubu bisa cika burin da suka daɗe suna mafarkinsa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa kwalejin kimiyya da fasaha ta tarayya a Gwarinpa, daya daga cikin manyan unguwannin Abuja, babban birnin kasar.

An ruwaito cewa wannan sabuwar makaranta za a sanya mata suna 'Bola Ahmed Tinubu Polytechnic' domin karrama mai girma shugaban kasa.

Shugaba Tinubu.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabuwar makarantar fasaha a Abuja Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa hakan na ƙunshe a wata wasika mai kwanan wata 16 ga Janairu, 2025, da aka aike wa ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta samu kudi sama da Naira biliyan 2 daga ɗaura aure a 2024

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaba Tinubu ya kafa sabuwar makaranta

Ministan ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta amince da kafa wannan kwalejin a Gwarinpa domin inganta horon fasaha, sana’o’i da dabarun kasuwanci bisa tsarin dokar ilimi ta kasa.

A cikin wasikar wadda Dakta Alausa ya sa hannu da kansa, ya nemi Wike ya bayar da shawarim wuraren da za a kafa makarantar na wucin gadi da na dindindin a Gwarinpa domin fara aiki.

Ministan ya kara da cewa kwararru daga ma’aikatar ilimi da hukumar kula da ilimin fasaha ta ƙasa (NBTE) za su ziyarci wuraren da aka bada shawarar domin duba su.

A cewarsa, bayan haka ne gwamnati za ta ɗauki matsaya kan wurin da za a gina makaranta bisa rahoton da tawagar za ta gabatar.

Shugaban AMAC ya yabawa Bola Tinubu

A nasa ɓangaren, shugaban karamar hukumar kwaryar birnin Abuja (AMAC), Christopher Zakka Maikalangu, ya yaba wa shugaba Tinubu bisa amincewa da kafa kwalejin a Gwarinpa.

Kara karanta wannan

Rikicin Tinubu da gwamnan Bauchi: Minista ya fadi dalilin rashin jituwa

A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai da al’amuran jama’a, Kingsley Madaki, ya fitar, Maikalangu ya nuna godewa ministan Abuja, Nyesom Wike.

Ya ce dole ne ya godewa Wike saboda rawar da ya taka wajen ganin wannan mafarkin ya zama gaskiya ga mazauna Abuja.

Maikalangu ya bayyana kafa Kwalejin Kimiyya da Fasaha a Gwarinpa a matsayin buri da ya zama gaskiya, wanda zai taimaka wajen kawo ci gaba ga mazauna birnin.

Tinubu ya fara ba ɗan Abuja minista a tarihi

Ya kuma ƙara da cewa a karon farko a tarihin kasar, wani ɗan asalin Abuja, Zaphaniah Bitrus Jisalo, ya zama minista a Najeriya.

Shugaban AMAC ya ce Bitrus Jisalo ɗan asalin Abuja ne kuma ya wakilci mazabar AMAC/Bwari a Majalisar wakilan tarayya na tsawon zango biyu.

Mace ta zama mataimakiyar shugaban DSS

A wani labarin, kun ji cewa mai girma shugaban ƙasa ya naɗa mace ta farko a matsayin mataimakiyar shugaban hukumar DSS ta ƙasa.

Kara karanta wannan

Maganar N Power ta dawo, Tinubu ya umarci sake fasalinta, matasa za su caɓa

Ma'aikatan hukumar ƴan sandan farin kaya da aka fi sani da DSS na yanzu da waɗanda suka riga suka ajiye aiki sun yaba da naɗin Folashade Arinola.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262