'Yan Bindiga Sun Yi Fitar Dango, Sun Kora Mazauna Kauyen Sakkwato cikin Daji

'Yan Bindiga Sun Yi Fitar Dango, Sun Kora Mazauna Kauyen Sakkwato cikin Daji

  • An samu rahoton cewa 'yan bindiga sun kai mummunan hari wani kauye a jihar Sakkwato tare da tafka muguwar sata
  • Ana zargin 'yan bindiga masu biyayya ga Kachalla Haru da Kachalla Chomo ne su ka shirya harin mai tayar da hankali
  • Sun sace mutanen da har yanzu ba a kai ga tattaro adadinsu ba, tare da jikkata wani matashi a kauyen Gado

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Sokoto - 'Wasu miyagun ‘yan ta’adda sun fantsama kauyen Sakkwato, su ka kaddamar da mummunan hari a kan jama’ar garin.

'Yan bindiga sun farmaki kauyen Gado da ke Unguwar Lalle, karamar hukumar Sabon Birni a jihar Sakkwato da sanyin safiyar Talata.

Sokoto
'Yan bindiga sun kai hari Sakkwato Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Zagazola Makama ya wallafa cewa miyagun mutanen sun hargitsa garin baki dayansa, yayin da ake jiran martanin hukumomi a kan lamarin.

Kara karanta wannan

An kama masu taimakon 'yan bindiga da kayan sojoji da 'yan sanda

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Yan bindiga sun sace mutanen Sakkwato

Miyagun ‘yan ta’adda sun kora mutanen kauyen Gado zuwa dazuka, kuma har yanzu ba a tantance yawan mutanen da aka sace ba.

‘Yan bindiga dauke da mugayen makamai sun kuma kwashe kayayyakin jama’a ciki har da dabbobi zuwa maboyarsu.

Sakkwato: ‘Yan bindiga sun sun addabi jama'a

Majiyoyin sun tabbatar da cewa maharan sun ji wa wani yaro rauni a lokacin harin kuma sun tilasta wa wasu mazauna kauyen tserewa zuwa dajin Sububu.

Ana zargin wasu gungun ‘yan bindiga karkashin jagorancin Kachalla Haru da Kachalla Chomo, shahararrun shugabannin ‘yan ta’adda da ke aiki a dajin Sububu, da kai harin.

'Yan bindiga sun sace amarya da kawayenta

A baya kun ji cewa an samu miyagun 'yan bindiga sun kai hari kauyen Sakkwato a lokacin da ake tsaka da biki, su ka sace amaryar da aka daura aurenta da kawayenta.

An zargi 'yan bindiga da ke mubaya'a ga Bello Turji da kitsa harin, su ka kutsa Kwaren Gamba kusa da kauyen Kuka Teke tare da dauke amaryar da karfin tsiya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.