'Yan Ta'addan ISWAP Sun Hallaka Babban Jami'in 'Yan Sanda a Borno

'Yan Ta'addan ISWAP Sun Hallaka Babban Jami'in 'Yan Sanda a Borno

  • Wasu ƴan ta'adda da ake zargin mayaƙan ƙungiyar ta'addanci ta ISWAP ne sun tafka sabuwar ta'asa a yankin Arewacin jihar Borno bayan sun kai hari
  • Ƴan ta'addan sun farmaki wani ma'aikacin lafiya wanda ya samu ya tsere tare da zuwa neman taimako wajen jami'an ƴan sanda
  • DPO na ƴan sanda tare da tawagarsa sun bi sahun ƴan ta'addan waɗanda suka yi musu kwanton ɓauna tare da hallaka babban jami'in tsaron

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Borno - Wasu da ake zargin ƴan ta'addan ƙungiyar ISWAP ne sun kashe wani babban jami'in ƴan sanda a yankin Arewacin jihar Borno.

Ƴan ta'addan na ISWAP sun kutsa cikin Sabuwar Marte da misalin ƙarfe 7:30 na yammacin ranar Litinin inda suka far wa wani ma’aikacin lafiya wanda ya yi sa’a ya tsere.

Kara karanta wannan

Dakarun sojoji sun sheke 'yan ta'adda 7, sun kwato makamai masu yawa a Kaduna

Mayakan ISWAP sun kashe dan sanda
'Yan ta'addan ISWAP sun hallaka DPO a Borno Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

Jaridar Daily Trust ta kawo rahoto cewa ma’aikacin lafiyar ya garzaya ofishin ƴan sanda domin sanar da su halin da ake ciki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƴan ta'addan ISWAP sun hallaka DPO

Lokacin da ya samu kiran gaggawar, DPO ɗin ya bi sawun ƴan ta’addan, amma abin takaici sai suka yi wa tawagar ƴan sandan kwanton ɓauna, rahoton jaridar Leadership ya tabbatar.

Wata majiyar tsaro ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa:

"A jiya ne ƴan Boko Haram suka shiga sabuwar Marte inda suka kashe DPO tare da raunata wasu mutum biyu."

Wata majiya wanda ɗan banga ne ya bayyana cewa:

"Wallahi abin takaici ne. Kwanaki mun rage masa hanya lokacin da muke dawowa daga Dikwa. Ya ce zai je ya ga iyalansa a Maiduguri."

Me ƴan sanda suka ce?

Legit Hausa tayi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ƴan sandan jihar Borno, Nahum Daso kan mummunan lamarin da ya faru.

Kara karanta wannan

'Yan Kwadago Sun Ƙara Daukar Zafi, Sun Ba Tinubu Wa'aɗi Ya Janye Ƙarin Kuɗin Wuta

Kakakin rundunar ƴan sandan ya bayyana cewa tabbas lamarin hallaka DPO ɗin ya faru.

Mayaƙan ISWAP sun farmaki manoma

A wani labarin kuma, kun ji cewa aƙalla mutane uku ne suka rasa ransu a wasu tagwayen hare-hare da mayaƙan ƙungiyar ta'addanci ta SWAP suka kai a ƙaramar hukumar Damboa ta jihar Borno.

Hakazalika wasu ƴan banga biyu sun rasa ransu samakon tashin abin fashewa a wani samame da dakarun soji suka kai yankin Kudancin Damboa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng