Badakalar N2.1trn: Jerin Tsofaffin Gwamnoni 54 da EFCC Ke Tuhuma Kan Zargin Almundahana

Badakalar N2.1trn: Jerin Tsofaffin Gwamnoni 54 da EFCC Ke Tuhuma Kan Zargin Almundahana

FCT, Abuja - Hukumar EFCC ta tabbatar da cewa ta na binciken zargin badakala da tsofaffin gwamnoni 54 suka yi a Najeriya.

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Ana zargin tsofaffin gwamnonin sun karkatar da N2.187trn a cikin shekaru 25 da aka yi tun bayan dawowa dimukradiyya.

Tsoffin gwamnoni 54 da EFCC ke tuhuma kan zargin almundahana
Hukumar EFCC na zargin tsoffin gwamnoni 54 da badakalar N2.187trn a Najeriya. Hoto: Ayodele Fayose, Yahaya Bello, Bello Matawalle.
Asali: Twitter

EFCC na zargin tsoffin gwamnoni 54

Kamar yadda Vanguard ta tattaro, ba a hada da sauran kadarori da aka kwato ba wanda yawan kuɗin ya kai biliyoyin Naira.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yawan kudi da ake zargin an sace ya kai kasafin kudin jihar Legas na shekarar 2024 (N2.25trn) sannan ya kai kasafin kudin dukkan jihohin Kudu maso Gabas guda biyar (N2.29trn).

Kara karanta wannan

"Buhari ya daura shugaban APC duk da zargin cin N15bn", Tsohon Minista ya tona asiri

Har ila yau, kudin ya fi kasafin kudin jihohin Arewa maso Gabas da kuma Arewa ta Tsakiya, cewar Journalist101.

Daga cikin tsoffin gwamnoni 58 wasu ana kan bincike yayin da wasu kuma aka kammala bincike da kuma hukunta su.

Tsoffin gwamnonin da EFCC ke zargi sun fito daga yankuna shida da muke da su a ƙasar daga Kudu har Arewa wanda suka haɗa da:

Tsoffin gwamnonin da EFCC ke zargi

1. Marigayi Abubakar Audu (N10.966 bn) - Kogi

2. TA Orji and 'ya'yansa (N551 bn) - Abia

3. Yahaya Bello (N80.2 bn) - Kogi

4. Chimaroke Nnamani (N5. 3 bn) - Enugu

5. Sullivan Chime (N450 million) - Enugu

6. Kayode Fayemi (N4bn) - Ekiti

7. Ayo Fayose (N6.9 bn) - Ekiti

8. Abdullahi Adamu (N15bn) - Nasarawa

9. Danjuma Goje (N5bn) - Gombe

10. Aliyu Wamakko (N15 bn) - Sokoto

Kara karanta wannan

Kaya na iya kara tsada sakamakon wani canjin kudin da Kwastam tayi

11. Sule Lamido (N1.35 bn) - Jigawa

12. Joshua Dariye (N1. 16 bn) - Plateau

13. Timipre Sylva (N19.2 bn). - Bayelsa

14. Saminu Turaki (N36bn) - Jigawa

15. Orji Uzor Kalu (N7. 6bn) - Abia

Sauran sun hada da:

16. Bello Matawalle (N70 bn) - Zamfara

17. Lucky Igbinedion (N4. 5 bn) - Edo

18. Rabi'u Kwakwanso (N10bn) - Kano

19. Peter Odili (N1000 bn) - Rivers

20. Jolly Nyame (N1.64 bn) - Taraba

21. James Ngilari (N167m) - Adamawa

22. Abdulaziz Yari (N84 bn) - Zamfara

23. Godswill Akpabio (N100bn) - Akwa Ibom

24. Abdul fatah Ahmed (N9 bn) - Kwara

25. Ali Mode-Sheriff (N300bn) - Borno

26. Willie Obiano (N43 bn) - Anambra

27. Ibrahim Dankwambo (N1. 3bn) - Gombe

28. Darius Ishaku (N39bn) - Taraba

29. Ramalan Yero (N700m) - Kaduna

30. Achike Udenwa (N350m) - Imo

Sai kuma:

Kara karanta wannan

Badakalar N80bn: Abin da wasu tsofaffin gwamnoni ke cewa game da Yahaya Bello

31. Rochas Okorocha (N10. 8bn) - Imo

32. James Ibori (N40 bn) - Delta

33. DSP Alamieyeseigha ((N2.655bn) - Bayelsa

34. Gabriel Suswam (N3. 111bn) - Benue

35. Samuel Orton (N107bn) - Benue

36. Murtala Nyako (N29bn) - Adamawa

37. Rashid Ladoja (4.7bn) - Oyo

38. Christopher Alao-Akala (N11. 5 bn) - Oyo

39. Marigayi Abdulkadir Kure (N600m) - Niger

40. Babangida Aliyu (N4bn) - Niger

Sannan akwai:

41. Abubakar Audu (N10bn) -. Kogi

42. Idris Wada (N500m) - Kogi

43. Ibrahim Shekarau (N950m) - Kano

44. Adamu Aliero (N10bn) - Kebbi

45. Usman Dakingari da matarsa (N5. 8bn) - Kebbi

46. Attahiru Bafarawa (N19. 6bn) - Sokoto

47. Jonah Jang (N6. 3bn) - Plateau

48. Aliyu Doma (N8bn) - Nasarawa

49. Tanko Al’Makura (N4bn) - Nasarawa

50. Boni Haruna (N93bn) - Adamawa

51. Bindow Jibrila (N62bn) - Adamawa

52. Adamu Muazu (13bn) - Bauchi

53. Isa Yuguda N212bn) - Bauchi

Kara karanta wannan

Sabon mafi karancin albashi: Gwamnoni sun yi wa ma'aikata kyakkyawan albishir

54. Mohammed Abubakar (N8. 5bn) - Bauchi.

EFCC ta yi garambawul a mukamai

Kun ji cewa Hukumar EFCC ta yi garambawul a muƙamai a kokarin kawo sauyi domin ci gaba da yaki da cin hanci a Najeriya.

Wannan nadin mukamai da sauye-sauye na zuwa ne yayin da hukumar ke tuhumar tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello kan badakalar N84bn.

Asali: Legit.ng

Online view pixel