Gwamnatin Tinubu Ta Sake Ajiye Tarihi, Mace Ta Samu Shugabancin NEMA Bayan Shekaru 25

Gwamnatin Tinubu Ta Sake Ajiye Tarihi, Mace Ta Samu Shugabancin NEMA Bayan Shekaru 25

  • Bola Ahmed Tinubu ya nada wanda za ta jagoranci hukumar NEMA kamar yadda sanarwa ta fito daga fadar shugaban kasa
  • Mai girma shugaban Najeriya ya zabi Zubaida Umar ta karbi ragamar NEMA wanda ta ke taimakawa da agajin gaggawa
  • A tarihin NEMA, sai a kan Zubaida Umar ne za a samu macen da ta taba darewa kan kujerar Darekta Janar tun shekarar 1999

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abuja - Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Najeriya ya amince da nadin sabuwar hukumar NEMA mai bada agajin gaggawa.

Zubaida Umar ta zama sabuwar Darekta Janar ta wannan hukuma mai taimakawa wajen kai agajin kar-ta-kwana a Najeriya.

NEMA DG
Bola Tinubu ya nada Zubaida Umar ta zama NEMA DG Hoto: @Dolusegun
Asali: Twitter

Hadimin Tinubu ya sanar da nadin NEMA-DG

Ajuri Ngelale ya sanar da haka a matsayinsa na mai magana da yawun shugaban kasa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Tinubu ya dauko mutumin Buhari ya ba shi shugabancin hukumar kula da almajirai

Kamar yadda Ajuri Ngelale ya bayyana a jawabin da ya fitar a ranar Juma’a, nadin ya nuna za a dama da kowane jinsi a mulki.

Bola Tinubu ya nada Zubaida Umar ne a lokacin da ake kukan mata ba su samun mukamai da kujeru a gwamnati a Najeriya.

Zubaida Umar: NEMA ta shiga karkashin mace

A tarihin hukumar NEMA da aka kafa tun 1999, ba a taba samun lokacin da mace ta jagorance ba sai a wannan karo.

Kamar yadda Olusegun Dada ya zayyano a dandalin X, sabuwar shugabar ta NEMA ta kware a bangarorin aiki da dama.

"Sabuwar Darekta Janar din ta shafe sama da shekaru 20 tana aiki a bangarori dabam-dabam,
Ciki akwai kula da ma’aikata, harkokin kudi da gudanarwa. Tana cikin ‘yan cibiyar kwararrun ma’aikatan banki da cibiyar ba da lamuni.
Tana da takardar shaidar ACCA a bangaren kula da dukiyar al’umma."

Kara karanta wannan

Rashin tsaro: Rundunar soji ta saduda, ta nemi agajin EFCC a wasu bangarori, ta fadi dalili

- Ajuri Ngelale

Ana sa ran kawo sauyi a NEMA

Da wannan sabon nadi da aka yi, tsohuwar darektar bankin ba da lamunin gina gidaje za ta shiga ofis ba da wata-wata ba.

Yayin da ta canji Ahmed Habib, Bola Tinubu ya ce yana fatan Zubaida Umar za ta kawo sauyi kamar yadda aka gani a FMBN.

Tinubu ya yi nade-naden mukamai

Rahoton nan ya tabbatar da mutane biyu suka samu mukami daga Kano a rana daya da Bola Tinubu ya tsige Hon. Sha’aban Sharada.

Nauyin kula da almajirai da marasa zuwa makarantun boko ya dawo hannun Janar Lawal Ja’afar Isa wanda ya yi gwamna a Kaduna.

Asali: Legit.ng

Online view pixel