Badakalar N37bn: Tsohuwar Ministar Buhari Za Ta Gurfana Gaban EFCC

Badakalar N37bn: Tsohuwar Ministar Buhari Za Ta Gurfana Gaban EFCC

  • Hukumar EFCC ta gayyaci tsohuwar ministar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari domin amsa tambayoyi
  • Hukumar ta gayyaci Sadiya Umar Farouq ne domin tatttaunawa da ita kan badaƙalar N37bn a lokacin tana minista
  • Sadiya a baya ta fito ta bayyana cewa ba ta da hannu a badaƙalar ta N37bn da ake zargin an haɗa baki da wani ɗan kwangila

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa ta'annati (EFCC), ta gayyaci tsohuwar ministar harkokin jin ƙai, Sadiya Umar-Farouq.

Hukumar ta gayyaci Sadiya ne kan cigaba da gudanar da bincike kan wasu maƙudan kuɗaɗe N37,170,855,753.44 da ake zargin an karkatar da su a hannunta ta hannun wani ɗan kwangila, James Okwete.

Kara karanta wannan

Hedikwatar tsaro ta bayyana nasarorin da sojoji suka samu a shekarar 2023

EFCC ta samu gayyata daga EFCC
Hukumar EFCC ta gayyaci Sadiya Farouk Hoto: Sadiya Umar Farouq CON, EFCC Nigeria
Asali: Facebook

EFCC ta gayyaci Sadiya

An buƙaci tsohuwar ministar da ta gurfana a gaban masu bincike a hedikwatar EFCC, Jabbi, Abuja a ranar Laraba, 3 ga watan Janairu, 2024, domin ta yi bayani kan badaƙalar zamba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jaridar The Punch ta ce hakan na ƙunshe ne a cikin wata takarda ta musamman da ta gani a ranar Asabar, 30 ga watan Disamba.

Wani ɓangare na takardar na cewa:

“Hukumar na binciken wani lamari ne da ya shafi karkatar da kuɗaɗe da ya shafi ma’aikatar kula da jin kai, bala’o’i da cigaban al’umma a lokacin da kike minista."
"Dangane da abin da ke sama, ana buƙatar da ki kawo kanki domin tattaunawa wacce aka tsara kamar haka: Laraba, 3 ga watan Janairu, 2024. Lokaci: Ƙarfe 10:00 na safe."

Me tsohuwar ministar ta ce?

An kasa samun tsohuwar ministar domin jin ta bakinta a ranar Asabar, saboda wayarta ta nuna cewa a kashe take.

Kara karanta wannan

Harin Plateau: Jam'iyyar PDP ta fadi laifin Tinubu, ta gaya masa muhimmin abu 1 da ya kamata ya yi

Da aka tuntuɓi tsohuwar mai taimaka mata kan harkokin yaɗa labarai, Nneka Ikem kan lamarin, sai ta kashe wayarta.

"Kamar yadda kake tambayata? Nima zan tambaye ka, a ina ka samu labarin cewa EFCC ta gayyace ta? Ikem ta tambaya kafin ta yanke kiran.

Kiraye-kirayen da aka ƙara yi mata ya nuna wayarta a kashe take.

A baya Umar-Farouq ta musanta sanin ɗan kwangilar, James Okwete, wanda har yanzu yana hannun hukumar EFCC.

EFCC Ta Fara Tuhumar Ministocin Buhari

A wani labarin kuma, hukumar EFCC ta fara tuhumar wasu ministocin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari kan badaƙalar N187bn.

Ministocin guda uku waɗanda suka yi aiki a ƙarƙashin gwamnatin Buhari, ana zarginsu ne da wawure dukiyar ƙasa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel