Mutane Sun Kama Lahaula Sakamakon Shirin Rusa Gidaje 677 Da Gwamnati Za Ta Yi

Mutane Sun Kama Lahaula Sakamakon Shirin Rusa Gidaje 677 Da Gwamnati Za Ta Yi

  • Hukumar gidaje ta tarayya tayi shiri tsaf domin a ruguza gine-gine fiye da 600 da aka yi a Amuwo-Odofin a Legas
  • Jami’an FHA sun tabbatar da cewa mutane sun rika yin gini a kan tituna da hanyoyin ruwa ba tare da umarni ba
  • Akwai gidaje sama da 700 da rushe-rushen zai shafa, ana sa ran hukuma ba za ta ruguza su daga sama har kasa ba

Lagos - Hukumar gidaje ta tarayya (FHA) ta shaida cewa ta shirya ruguza gidaje 677 a sakamakon sabawa doka da aka yi wajen gina su.

Bayan wadannan gidaje da za a rusa har kasa, hukumar ta FHA za ta yi wasu ‘yan rushe-rushe da za su shafi wasu gidaje akalla 744.

Gidaje
Gidaje a Legas Hoto: Getty Images/Andrew Esiebo
Asali: Getty Images

Kamar yadda The Guardian ta kawo rahoto, za a ayi wannan aikin rusau ne a unguwar FESTAC a yankin Amuwo-Odofin a Legas.

Kara karanta wannan

Mataimakin Sanusi a bankin CBN ya fito ya soki hukuncin zaben gwamnan jihar Kano

Shugaban FHA na shiyyar Kudu maso yamma, Akintola Olagbemiro ya yi wannan bayani lokacin da ya ziyarci unguwar da za ayi aikin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mista Akintola Olagbemiro ya je Amuwo-Odofin domin ganin yadda mutane su ka yi watsi da tsarin hukuma wajen gina gidajen na su.

An yi gine-ginen gidaje babu umarni

Jami’in yake cewa duk da wasiku da ziyarar da aka rika kai wa masu ruwa da tsaki, mutane sun cigaba da aikin gine-gine babu ka’ida.

Daily Post ta ce an zargi masu gidajen da yin gini a kan ruwa ba tare da bin dokoki ba.

A cewar Olagbemiro, jama’a sun rika shiga cikin filayen Festac ba tare da ka’ida ba, sun yi gine-gine barkatai a wuraren da bai dace ba.

Shirin da hukumar FHA ta ke yi

Jami’in ya kara da FHA na kokarin ganin sun gano yadda za a magance matsalar shiga filin gwamnati domin a rayu cikin natsuwa.

Kara karanta wannan

Jerin manyan motocin karau da ake zargin tsohon Gwamnan CBN Emefiele ya siya da N1.2bn na kudin kasa

Mataimakiyar Manajar FHA ta Kudu maso yamma, Francisca Michael-James ta ce za su bukaci jami’an tsaro domin fara rusa gine-gine.

Francisca Michael-James take cewa akwai ginin da aka yi a kan tituna da hanyoyin ruwa.

Abin da za a fara yi shi ne a rusa bangaren gine-ginen domin a fitar da hanya, hakan zai shafi gidaje 1, 421 da za a ruguza ko za a taba.

Za a gyara gidaje a Aso Rock

Watanni 5 da hawa mulki, sai ga labari cewa Shugaban Najeriya zai batar da kusan N10bn a kan gyaran gidajen da su ke kwana a ciki.

Sannan za a gyara wani gidan shugaban kasa da ke Legas duk da fadar shugaban kasa ta koma Abuja shekaru fiye da 30 da suka wuce.

Asali: Legit.ng

Online view pixel