NDLEA Ta Kama Wata Mata da Tulin Haramtattun Kwayoyi a Filin Jirgin Kano

NDLEA Ta Kama Wata Mata da Tulin Haramtattun Kwayoyi a Filin Jirgin Kano

  • Jami'an hukumar NDLEA sun cafke wata mai suna Bilkisu ɗauke da ƙunshin holar iblis sama da 50 a filin jirgin Aminu Kano
  • A wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce an kama matar ne yayin da take shirin kama jirgi zuwa ƙasa mai tsarki ranar Talata
  • NDLEA ta ƙara da bayyana yadda ta kama wasu da haramtattun kwayoyi a jihar Oyo da titin Bauchi zuwa Gombe

Jihar Kano - Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA) ta damƙe wata mata ɗauƙe da ƙunshin hodar iblis 52 a filin sauka da tashin jiragen sama na Aminu Kano a jihar Kano.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa NDLEA ta kama matar mai suna, Bilkisu Mohammed Bello, yayin da take yunkurin kama jirgi zuwa ƙasar Saudiyya.

Hukumar NDLEA ta kama mace da hodar iblis a Kano.
NDLEA Ta Kama Wata Mata da Tulin Haramtattun Kwayoyi a Filin Jirgin Kano Hoto: @NDLEA
Asali: Twitter

A wata sanarwa da Daraktan yaɗa labarai na hukumar NDLEA, Femi Babafemi, ya fitar, ya ce jami'ai sun cafke matar da ake zargin ne tun ranar Talata.

Kara karanta wannan

Soyayyar Damfara: Baturiya Ta Bayyana Yadda Dan Yahoo Yahoo Ya Damfare Ta Kudi Har N122m

Sanarwan ta ce:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"A yayin da ake zantawa da ita, ta amsa cewa kwalayen hodar iblis da aka ba ta ta hadiye kafin lokacin tashin jirgin nata an ajiye su ne a wani gida da ke unguwar Farawa a Kano."
"Lokacin da ta jagoranci jami'an hukumar NDLEA zuwa gidan, an samu ƙunshi 52 na haramtattun kayan da nauyinsu ya kai giram 767."

Wasu nasarorin da NDLEA ta samu a Najeriya

Haka nan kuma sanarwan ta ƙara da bayyana wasu nasarorin da jami'an hukumar NDLEA suka samu a wasu sassan jihohin Najeriya.

A rahoton jaridar PM News, sanarwan NDLEA ta ƙara da cewa:

“Haka nan kuma, an kama wani da ake zargi mai suna, Auwal Bindow, a kan titin Bauchi zuwa Gombe ranar Juma’a ɗauke da maganin turamol 50,000."
"A jihar Oyo, jami’an NDLEA da ke sintiri a titin Legas zuwa Ibadan, sun kama Anuoluwapo Blessing Iyanu, mai shekaru 32, da kwalaye 52 na wiwi sativa mai nauyin kilogiram 30 a ranar Laraba 4 ga watan Oktoba."

Kara karanta wannan

"Akwai Babban Abin Damuwa" INEC Ta Bayyana Abinda Ta Hango Zai Kawo Cikas a Zaɓen Gwamnoni 3

Babban Jigon APC Ya Yi Murabus, Ya Fice Daga Jam'iyyar Zuwa Tsagin Adawa

A wani rahoton na daban kuma Jam'iyyar APC ta rasa ɗaya daga cikin manyan jiga-jiganta a jihar Kogi yayin da zaɓen gwamna ke ƙara kusantowa a wata mai zuwa.

Yahaya Ododo, ya yi murabus daga mamban jam'iyyar APC, kana ya koma AA domin mara wa ɗan takarar jam'iyyar baya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel