Ba Za Ta Yi Wu Ba: Tinubu Ya Ce Dole a Bijirewa Turbar Da Buhari Ya Daura Najeriya

Ba Za Ta Yi Wu Ba: Tinubu Ya Ce Dole a Bijirewa Turbar Da Buhari Ya Daura Najeriya

  • Bola Ahmed Tinubu ba zai lamunta da yadda ake kashe duk abin da ya shigo aljihu a biyan bashi ba
  • Gwamnatin baya ta karbo aron makudan kudi a gida da waje, hakan ya jawo ake fama da bashi
  • Shugaba Tinubu ya tabbatar da cewa gwamnatinsa ba za ta karar da arziki kasa a kan basoshin ba

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Abuja - Bola Ahmed Tinubu ya nuna ba zai amince da tsarin da ake tafiya a kai na kashe kusan duka lalitar gwamnati wajen biyan bashi ba.

A ranar Lahadi, Daily Trust ta rahoto Shugaban Najeriyan ya na sukar yadda kudin-shiga su ke karewa duk a biyan bashin kudin da aka aro.

Mai girma Bola Ahmed Tinubu ya bayyana haka da ya halarci bikin bude taron kungiyar lauyoyi na NBA da aka yi a filin wasan MKO Abiola.

Kara karanta wannan

Idan Na Nemi Fili Ka da a Yanka Mani – Tinubu Ya Fadawa Wike Abin da Yake So a Abuja

Bola Tinubu
Bola Tinubu da Jakadan Ali Bongo Ondimba Hoto: @PBATMediaCentre
Asali: Twitter

Jawabin Shugaban kasa Bola Tinubu

"Za mu cigaba da kashe 90% na kudin shiganmu wajen biyan bashin kudi a kasashen waje? Hanyar hallaka ce. Ba za ta yiwu a cigaba ba.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Tilas mu kawo sauyin da su ka zama dole ga kasarmu, sai mun farka daga gyangyadin da mu ke yi sai girmama mu a kasashen duniya."

- Bola Tinubu

Shugaban kasar ya gabatar da jawabi mai ban sha’awa a gaban lauyoyi 16, 190 da ke halartar gagarumin taron da aka saba yi a duk shekara.

A wajen ne shugaban kasar ya shaida cewa da farko za a koka da manufofin da ya fito da su, amma ya tabbatar da za a ga amfaninsu nan gaba.

Punch ta rahoto Bola Tinubu ya na mai cewa saboda yaran da za a haifa nan gaba ya fito da tsare-tsaren da wasu su ke kokawa da su a Najeriya.

Kara karanta wannan

Ana tsaka mai wuya: Abin da Tinubu ya fadawa Malaman addini kafin su tafi Nijar

"Dole mu yi abin da za mu yi domin kai kasar nan ta cin ma burinta. Ba batun ni ko ku ake yi ba, ana maganar al’umma masu zuwa ne nan gaba."

- Bola Tinubu

A cewarsa, Gwamnatinsa za ta kawo irin sauyin da aka gani a bangaren shari’a a lokacin da ya yi gwamna na tsawon shekaru takwas a Legas.

Tony Elumelu ya yabi manufofin Tinubu wanda ya gaji bashin kudi masu yawa daga hannun gwamnatin Muhammadu Buhari a karshen Mayu.

Tinubu bai son filaye a Abuja

Rahoton da mu ka samu a baya shi ne Shugaban Najeriya ya nuna bai bukatar a raba masa filaye a Abuja, sai dai ayi wa al’umma aikin da za a mora.

Mai girma shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bukaci ministansa watau Nyesom Wike ya gaggauta kammala aikin titin jirgin kasan birnin Abuja.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng