'Yan Bindigan Da Suka Sace Babban Basarake a Abuja Sun Nemi N9m a Matsayin Kudin Fansa

'Yan Bindigan Da Suka Sace Babban Basarake a Abuja Sun Nemi N9m a Matsayin Kudin Fansa

  • Bayan shafe kwanaki a hannunsu, ƴan bindiga sun kira waya domin neman kuɗin fansar basaraken da suka sace a birnin tarayya Abuja
  • Ƴan bindigan sun nemi da a biya su kuɗin fansa har N9m na dagacin ƙauyen Ketti da kuma wasu mutum biyu da suka haɗa da su
  • Hadimin basaraken shine ya tabbatar da neman kuɗin fansan da ƴan bindigan suka yi bayan sun tuntuɓi iyalansa

Abuja - Miyagun ƴan bindigan da suka sace dagacin ƙauyen Ketti a ƙaramar hukumar Abuja Municipal (AMAC), Cif Sunday Zakwoyi, da wani hadiminsa, Markus Gade, sun nemi kuɗin fansa.

Ƴan bindigan waɗanda suka haɗa da kuma a wani mazaunin ƙauyen a lokacin farmakin, sun buƙaci da a basu N9m a matsayin kuɗin fansa, rahoton Daily Trust ya tabbatar.

Kara karanta wannan

Gwamna Uba Sani Ya Tona Asirin Wasu Gwamnoni da Suka Rika Ma'amala da Yan Ta'adda a Jihohinsu

Yan bindiga sun nemi N9m kudin fansar basaraken Abuja
'Yan bindigan sun bukaci N3m kan kowane mutum daya Hoto: Guardian.com
Asali: UGC

Rahotanni sun tabbatar da cewa da safiyar ranar Juma'a da ta gabata, ƴan bindigan suka dira a fadar basaraken sannan suka yi awon gaba da shi tare da hadiminsa da wani mutum ɗaya.

Ƴan bindigan sun kira waya

Wani hadimin basaraken wanda ya nemi da a sakaya sunansa, ya bayyana a ranar Talata cewa shugagan ƴan bindigan ya kira waya a ranar Lahadi, ta hannun wayar ɗaya daga mutanen da suka sace.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Hadimin ya bayyana cewa shugaban ƴan bindigan ya tuntuɓi ɗaya daga cikin iyalan basaraken inda ya buƙaci da a biya N3m kan kowane mutum ɗaya da suka sace waɗanda ke tsare a hannunsu.

Har ya zuwa yanzu dai, kakakin rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja, DSP Josephine Adeh, bata yi ƙarin haske ba akan lamarin.

Ƴan bindiga a cikin ƴan kwanakin nan suna matsawa yankunan da ke a birnin tarayya Abuja, inda suke shiga suna cin karensu babu babbaka, tare da yin awon gaba da mutanen da basu ji ba basu gani ba.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: INEC Ta Saki Jerin Sunayen 'Yan Takarar Gwamna a Jihohin Kogi, Bayelsa Da Imo

Yan Bindiga Sun Sace Mutum Hudu a Birnin Tarayya Abuja

A wani labarin na daban kuma, kun ji cewa ƴan bindiga sun yi awon gaba da wasu mutum huɗu a birnin tarayya Abuja.

Ƴan bindigan sun dira ne a yankin Mpabe na Abuja inda suka riƙa bin gida-gida sna tasa ƙeyar mutanen da suka zo ɗauka.

Asali: Legit.ng

Online view pixel