‘A Kame Atiku da Obi’: Fani-Kayode Ya Yi Martani Kan Zargin Kafa Gwamnatin Wucin Gadi

‘A Kame Atiku da Obi’: Fani-Kayode Ya Yi Martani Kan Zargin Kafa Gwamnatin Wucin Gadi

  • Ana ci gaba da cece-kuce kan ikrarin hukumar DSS na cewa, akwai masu kitsa hanyar kafa gwamnatin wucin gadi a Najeriya
  • Femi Fani-Kayode ya yi tsokaci, ya ce kawai a kama Peter Obi na jam’iyyar Labour da kuma Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP
  • A rubutun da ya yada a Twitter, Kayode ya ce babu mamaki akwai hannun ‘yan jam’iyyar adawa a wannan shiri na kawo gwamnatin wucin gadi

Jigon jam’iyyar APC, Femi Fani-Kayode ya yi kira ga kama ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun PDP da Labour; Atiku Abubakar da Peter Obi.

Tsohon ministan ya bayyana hakan ne a martaninsa ga batun hukumar DSS na ranar 29 ga watan Maris na cewa akwai masu son kawo tsaiko ga gwamnati mai jiran gado.

A cewarsa, zargin kafa gwamnatin wucin gadi ba zai rasa nasaba da Atiku da Obi ba, don haka ya kamata a gaggauta kama su, rahoton Vanguard.

Kara karanta wannan

IPAC Ta Yi Martani Yayin da DSS Ta Gano Masu Yunkurin Kafa Gwamnatin Wucin Gadi

Kayode ya caccaki Atiku da Obi
Femi Fani-Kayode kenan na APC | Hoto: dailypost.ng
Asali: UGC

Ya nemi a kwamushe manyan ‘yan siyasa, Obi da Atiku

Kayode, a wani rubutun da ya yada a Twitter a ranar Alhamis, ya ce bai kamata a dauki batun da DSS din ta gabatar sako-sako ba saboda muhimmancinsa.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A cewarsa, duk da ba a kafa gwamnatin wucin gadin ba, akwai yiwuwar a samu tsaiko da jefa Tinubu cikin barazana kafin rantsar dashi.

A cewarsa:

"A yanzu dai alamomin a bayyane suke kuma balo-balo cewa akwai wani sharri a kasa.
“Abin yabawa ne da kuma jinjinawa cewa DSS tana aikinta, daga karshe kuma ta ba da sanarwa jiya na abin da ke faruwa.”

A tun farko, hankali ya tashi bayan samun labarin yadda wasu ‘yan siyasa ke neman kawo gwamnatin wucin gadi kafin rantsar da Tinubu.

PDP da APC sun ce a bayyana sunayen masu kitsa sharrin

Kara karanta wannan

Gwamnatin wucin gadi: PDP da APC sun ba DSS shawarin wasu 'yan siyasa a Najeriya

A bangare guda, jam’iyyun siyasan APC da PDP sun ce lokaci ya yi da DSS ya kamata ta sanar da duniya wadanda ke shirin kawo tsaiko ga tsarin.

Hakazalika, sun nemi a kama duk wani dan siyasa da ake zargin yana da hannu a tunanin kawo gwamnatin wucin gadin.

Wannan na bayyana cewa, jam’iyyun basu amince daya daga cikin mambobinsu ne mai kokarin kawo wannan lamari ga kasar nan ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.