2023: Jerin Jihohi 28 da Za a Yi Zaben Gwamnoni a Najeriya a Ranar Asabar

2023: Jerin Jihohi 28 da Za a Yi Zaben Gwamnoni a Najeriya a Ranar Asabar

  • Yayin da zaben gwamnoni ya gabato, yana da muhimmanci a san adadin jihohin da za a yi zabe a Najeriya
  • Akalla akwai jihohi 28 da za a kada kuri’u a gobe Asabar 18 ga watan Maris a Najeriya bayan dage zaben daga 11 ga watan na Maris
  • Rahoto ya bayyana wadannan jihohin da kuma wasu jihohin da ba za a yi zaben gwamna ba a ranar ta Asabar

Najeriya - Bayan kammala zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya, sakamako daga hukumar zabe ta INEC ya fito, wadanda basu ci zabe ba sun bayyana tafiya kotu.

Baya ga haka, sauran zaben jihohi; inda za a zabi sabbin gwamnoni ko kuma masu komawa da kuma ‘yan majalisun dokoki na jiha.

‘Yan Najeriya za su fito ne domin kada kuri’unsu a ranar Asabar 18 ga watan Maris, bayan dage zaben daga ranar 11 ga watan na Maris.

Kara karanta wannan

Sakamakon Zaɓen Gwamnoni Na 2023: Jerin Zaɓaɓbun Gwamnoni 5 Da Suka Ci Zaɓe Da Ƙuri'u Mafi Ƙaranci

Jihohin da za a kada kuri'u a Najeriya
Hoton mata na kada kuri'arta a rumfar zabe | Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

Gaba daya, jam’iyyun siyasa 18 ne ke da ‘yan takarar gwamna da ‘yan majalisu a Najeriya, ba a dukkan jihohin kasar bane kuma za a yi zaben.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dalilin da yasa wasu jihohin ba za a yi zabe ba

A bayyane yake, akwai jihohi 28 da za a kada kuri’u a Najeriya cikin 36 saboda akwai jihohin da zabensu ya bambanta da saura.

Kamar jihohin Anambra, Bayelsa, Edo, Ekiti, Imo, Osun da Ondo, duk suna da lokutan yin zabensu na daban ba na ranar Asabar mai zuwa ba.

Samun mabambantan lokacin zabe a jihohin yana da nasaba da hukunce-hukuncen kotu da suka sanya ake yin zaben daban.

Sai dai, zaben ‘yan majalisun jihohi a tare ake yi, kuma za a zabi ‘yan majalisu 993 a fadin jihohin Najeriya, kamar yadda bayanan INEC suka nuna.

Kara karanta wannan

Karin bayani: INEC ta fadi ranar da za a karasa zaben da ba a kammala ba a Najeriya

Jihohin da za a yi zaben gwamnoni a Najeriya

  1. Abia
  2. Adamawa
  3. Akwa Ibom
  4. Bauchi
  5. Benue
  6. Borno
  7. Kuros Riba
  8. Delta
  9. Ebonyi
  10. Enugu
  11. Gombe
  12. Jigawa
  13. Kaduna
  14. Kano
  15. Katsina
  16. Kebbi
  17. Kwara
  18. Legos
  19. Nasarawa
  20. Neja
  21. Ogun
  22. Oyo
  23. Filato
  24. Ribas
  25. Sokoto
  26. Taraba
  27. Yobe
  28. Zamfara

An tura EFCC jihohin Kano, Jigawa da Katsina

A jajiberin zabe, hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ta bayyana tura jami’anta bangarori daban-daban na jihohin Kano, Katsina da Jigawa.

Wannan na zuwa ne a shirin hukumar na tabbatar da an yi zabe cikin tsanaki a jihohin da ke Arewa maso Yamma a Najeriya.

An samu hargitsi a zaben shugaban kasa da aka yi a wasu jihohin Najeriya, ciki har da jihar Kano.

Asali: Legit.ng

Online view pixel