Hukumar Zabe Ta INEC Ta Ce Za a Kammala Sauran Zabukan Najeriya da Suka Rage a Ranar 15 Ga Afrilu

Hukumar Zabe Ta INEC Ta Ce Za a Kammala Sauran Zabukan Najeriya da Suka Rage a Ranar 15 Ga Afrilu

  • Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta sanya ranar karasa zabukan da aka yi ba a kammala ba a Najeriya
  • A ranar 15 ga watan Afrilu ne za a karasa zabukan, kamar yadda INEC ta bayyana a yau Litinin 27 ga watan Maris
  • An samo tsaiko a wasu bangarori daban-daban an Najeriya, an soke sakamako, an kuam dage sanar da sakamakon zabe

FCT, Abuja - Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta sanya ranar da za ta kammala zabukan da suka rage ba a yi su ba a Najeriya na bana.

Hukumar ta ce, za a kammala sauran zabukan gwamna, na ‘yan majalisun tarayya da na jihohi ne a ranar 15 ga watan Afrilu mai zuwa.

Idan baku manta ba, an samu tsaiko a Najeriya, har ta kai aka dage zabe ko soke shi a wasu yankuna daban-daban na kasar nan.

Kara karanta wannan

INEC Tayi Watsi da Kiraye-Kiraye, Ta Tsaida Ranar Rabawa Zababbun Gwamnoni Satifiket

INEC ta ce za a sake zabe a wasu yankunan Najeriya
Shugaban hukumar zabe ta INEC, Mahmud Yakubu | Hoto; dailypost.ng
Asali: UGC

A wasu yankuna da jihohin a Najeriya, an samu tsaikon da ya kai ga zubar da jini, misali kamar jihar Taraba da ke Arewa maso Gabashin Najeriya.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Abin da INEC ke cewa game da sake zabe a wasu yankuna

A sanarwar da INEC ta fitar a ranar Litinin 27 ga watan Maris, ta ce:

“A taron da ta gudanar a yau, hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta yanke shawarar cewa za a gudanar da dukkan zabukan gwamnoni, na ‘yan majalisun tarayya da na jihohi da ba a yi ba a a ranar Asabar 15 ga Afrilu, 2023.”

Ya zuwa yanzu, hukumar bata bayyana sanarwar inda za a yi zaben ba a hukumance, amma ta ce za ta ba da bayani nan ba da jimawa ba.

INEC ta ayyana sakamakon zaben Adamawa ‘Inconclusive’

Kara karanta wannan

Zaben 2023: "Abin Da Yan Adawa Suka Shirya Yi Yayin Rantsar Da Ni", Tinubu Ya Yi Fallasa, Ya Ambaci Sunaye

A wani labarin, kuma zabe mai zaman kanta ta bayyana cewa, bata amince da sakamakon zaben jihar Adamawa da aka gabatar mata ba a makon da ya gabata.

Wannan ya faru ne sakamakon tsaiko da jinkirin da aka samu wajen tattara sakamakon zaben da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris da muke ciki.

Hukumar ta bayyana cewa, za a sake yin zaben a wasu yankunan jihar, inda ta bayyana cewa za ta sanar da lolacin bayan duba cikin tsanaki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.