Allah Ya Yiwa Na'ibin Limamin Masallacin Sultan Bello Rasuwa

Allah Ya Yiwa Na'ibin Limamin Masallacin Sultan Bello Rasuwa

  • Allah ya yiwa mataimakin limamin masallacin Sultan Bello Kaduna, Mallam Ibrahim Isa, rasuwa
  • Marigayin ya rasu ne da safiyar ranar Laraba a wani asibiti a cikin birnin Kaduna, bayan rashin lafiya
  • Kwamitin masallacin ya bayyana cewa za a yi masa sallar Jana'iza a harabar masallacin bayan an gudanar da Sallar Azahar

Jihar Kaduna- Mataimakin limamin masallacin Sultan Bello dake Kaduna, Mallam Ibrahim Isa, ya rigamu gidan gaskiya.

Allah ya yiwa Mallam Ibrahim Isa Rasuwa ne da safiyar ranar Laraba a asibitin Garkuwa dake cikin birnin Kaduna, bayan yayi fama da rashin lafiya. Rahoton Daily Trust.

Na'ibi
Allah Ya Yiwa Na'ibin Limamin Masallacin Sultan Bello Rasuwa Hoto: Facebook/ Masallacin Sultan Bello Kaduna
Asali: Facebook

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Kwamitin masallacin Sultan Bello na Kaduna, ya sanar a shafin sa na Facebook cewa za a gudanar da sallar Jana'izar mamacin ne bayan sallar Azahar a harabar masallacin na Sultan Bello.

Kara karanta wannan

2023: Shugaban APC Na Kasa Ya Fasa Kwai, Ya Ce Zaben Shugaban Kasa Yana da Naƙasu

Sanarwar na cewa:

“Tare da yarda da ƙaddarar Allah maɗaukakin Sarki, muna sanar da rasuwar mataimakin limamin mu, Mallam Ibrahim Isa, wanda ya rasu yau (Laraba) da safe a asibitin Garkuwa."
“Za a gudanar da Sallar Jana'izar sa a harabar masallacin bayan Sallar Azahar. Allah Ubangiji yayi masa rahama ya sanya Aljannah Firdausi ta zama makoma a gare sa."

Ko a baya an yi babban rashi a Kaduna

Ko a cikin ƴan kwanakin nan da suka gabata an yi wani babban rashi a jihar Kaduna.

Mahaifiyar sanannen malamin addinin musuluncin nan, Sheikh Ahmed Abubakar Gumi, ta rasu. Mahaifiyar malamin addinin musuluncin ta rasu ne a ranar Lahadi, 5 ga watan Fabrairun 2023 a wani asibiti a birnin tarayya Abuja.

An gudanar da jana'izar ta kamar yadda addinin musulunci ya tanada a ranar Litinin 6 ga watan Fabrairun 2023, a cikin birnin Kaduna.

Sheikh Ahmed Abubakar Gumi dai yana gudanar da karatuttukan sa a masallacin Sultan Bello dake Kaduna.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Tarihin 'yan takara gwamna biyu na APC da PDP a jihar Arewa mai daukar hankali

Malaman Musulunci Sun ba Tinubu, Zababbun Shugabanni Shawara Kafin Shiga Ofis

A wani labarin na daban kuma, malaman addini da dama sun janyo hankali zaɓaɓɓun shugabanni a ƙasar nan.

Cibiyar addinin musulunci ta ICICE, itace ta shirya wata lakca ta musamman domin janyo hankalin zaɓaɓɓun shugaban kan nauyin da ya rataya a wuyan su na al'umma.

Asali: Legit.ng

Online view pixel