Tinubu Ya Shigar da Kara Domin Hana Jam’iyyar Labour da PDP Dakatar da Tattara Sakamakon Zabe

Tinubu Ya Shigar da Kara Domin Hana Jam’iyyar Labour da PDP Dakatar da Tattara Sakamakon Zabe

  • Bola Ahmad Tinubu ya tafim kotu don dakatar da yunkurin 'yan PDP da LP wajen tabbatar da an tsaya da batun tattara sakamakon zaben bana
  • Tinubu da Shettima sun ce dakatar da tattara sakamakon zabe zai jawo asara, don haka a ci gaba don gano wanda ya ci zabe
  • A gege guda, Tinubu ne ya lashe zaben shugaban kasa a jihar Borno, ya fi Atiku da kur'u sama da 60,000

Jihar Kano - Bola Ahmad Tinubu, tsohon gwamnan jihar Legas ya shigar da kara hukumar zabe ta INEC da Action Alliance don dakatar da jam’iyyar Labour da PDP daga yunkurin hana ci gaba da tattara sakamakon zaben bana.

Tinubu, wanda shine dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya ce sam ba zai bari a dakatar da tattara sakamakon da ya hango zai kaishi Villa ba a zaben na bana.

Kara karanta wannan

Ku rungumi kaddara: Tinubu ya tura sako mai daukar hankali ga Atiku da Peter Obi

Idan baku manta ba, an yi zaben shugaban kasa a Najeriya a ranar 25 ga watan Faburairu, kuma Tinubu ke kan gaba a yawan kuri’u.

Tinubu ya kai kara kotu kan batun dakatar da sakamakon zabe
Dan takarar shugaban kasa na APC, Bola Ahmad Tinubu | Hoto: vanguardngr.com
Source: Facebook

Karar da Tinubu ya shigar

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin karar da ya shigar a Kano mai lamba FHC/KN/CS/43/2023, an ambaci INEC da Action Alliance a matsayin wadanda ake kara, Daily Trust ta ruwaito.

Hakazalika, abokin takararsa, Kashim Shettima ne mutum na biyu bayan shi a wadanda ke shigar da kara a gaban kotun tarayyar da ke Kano.

A karar, Tinubu da Shettima sun nemi kotu da ta hana kawo tsaiko ko dakatar da tattara sakamakon zaben da tuni an fara nisa.

A cewarsu, dakatar da tattara sakamakon zai jawo asara mai yawa ga wadanda suka shigar da kara matukar aka bi ta su PDP da LP aka dakatar, Punch ta ruwaito.

A halin da ake ciki, har yanzu ana ci gaba da tattara sakamakon zaben shugaban kasa na 2023, kuma alamu sun nuna Tinubu ya fi yawan kuri’u a jihohin da aka sanar.

Kara karanta wannan

2023: "Rayuwa Ta Na Cikin Hatsari", Baturen Zabe Na Jihar Rivers Ya Dakatar Da Tattara Sakamakon Zabe

Tinubu ya lashe Borno

A wani labarin, kunji yadda Bola Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa a jihar Borno da ke Arewa maso Gabas.

Ya samu kuri'u sama da 250,000, inda ya ba Atiku na jam'iyyar APC kuri'u sama da 60,000 a zaben bana a jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng