Yan Ta'adda Sun Kai Hari Rumfar Zabe, Sun Banka Wa Akwatin Zabe Wuta

Yan Ta'adda Sun Kai Hari Rumfar Zabe, Sun Banka Wa Akwatin Zabe Wuta

  • Wasu yan daban siyasa dauke da bindigu da muggan makamai sun kai wasu wasu rumfunan zabe a Jihar Legas
  • Rahotanni sun nuna cewa wuraren da abin ya shafa sun hada da unguwar Oshodi da Otire, inda maharan suka fatattaki jama'a kafin suka kona akwatin zabe
  • Majiyoyi sun bayyana cewa yan ta'addan sun kai hare-haren ne yan mintuna bayan da jami'an tsaro masu aikin zabe suka bar rumfunan zaben

Jihar Legas - Wasu yan daba dauke da bindigu sun kai hari rumfunan zabe a Oshodi da Itire a Legas, inda suka kona akwatunan zabe.

Daily Trust ta rahoto cewa maharan sun taho ne sanya da bakaken tufafi da face mask misalin karfe 11.30 na safiyar ranar Asabar.

Rumfar zabe
Motar yan sanda a rumfar zabe. Hoto: @daily_trust
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Bayan gama da tara kuri'u, 'yan daba sun kone akwatunan zabe

Wasu masu zabe da ba su iya tserewa ba a lokacin da yan daban suka iso sun jikkata.

Wasu majiyoyi sun ce yan ta'addan sun kai farkamin ne yan mintuna bayan jami'an tsaro da ke aikin zabe sun bar wuraren.

A cewar wani Tajudeen Haruna, bayan yan mintuna, yan daban sun bude wuta don tsorata masu zabe.

Ya cigaba da cewa:

"Daga baya ne yan ta'addan suka cinna wa akwatin zaben da sauran kayan zabe wuta."

Hakazalika, wasu yan ta'adda sun kai hari a unguwar Itire, misalin karfe 12 na rana, suka tsorata mutane da masu zabe a yankin.

James Nwoke, ya yi ikirarin cewa an yi hakan da gangan ne don haka wasu mutane zabe.

Amma, akwai yan sanda da dama da sojoji a birnin Legas a ranar Asabar don kiyayye rushewar doka da oda.

A bangare guda, wasu matasa sun mayar da hanyar Agege da Apapa-Oshodi da wasu yankunan Ago palace zuwa filin kwallo.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: An Cafke Mutum 15 A Katsina Kan Zargin Canja Alkalluman Zabe

Ana zullumi a mafi yankuna da ke Ago, Isolo da Ire-Akri bayan wasu sun gaza gana akwatunan zaben su.

An kama wani mutum dauke da miliyoyin naira na sabbi da tsaffin kudi zai kai wa dan siyasa a Gombe

A wani rahoton kun ji cewa hukumar yaki da rashawa na ICPC ta kama wani Hassan Ahmed da makuden takardun naira da suka hada da sabbi da tsaffi a yayin da al'umma ke fama da karancin kudi.

Sojoji na 33 Artillery Brigade da ke aikin sintiri a Alkaleri Bauchi ne suka damke mutumin da kudaden cikin jaka ta 'Ghana must go' sannan suka kai shi wurin ICPC.

Asali: Legit.ng

Online view pixel