Hotunan Wani Jami'in Sojan Bogi Da NSCDC Ta Kama a Nasarawa Yana Damfarar Mutane

Hotunan Wani Jami'in Sojan Bogi Da NSCDC Ta Kama a Nasarawa Yana Damfarar Mutane

  • Dubun wani mutum mai yi wa dakarun sojojin Najeriya sojan gona a jihar Nasarawa yana karban kudi hannun jama'a a cika
  • Jami'an hukumar tsaro ta NSCDC ne a Nasarawa suka kama Moses Ayaka, dan shekara 32 a Lafia, babban birnin jihar Nasarawa
  • Ayaka, a yayin da ake masa tambayoyi bayan kama shi ya amsa cewa ya damfari mutane kudin da ya tasanma N440,000 a jihar

Jihar Nasarawa - Jami'an hukumar tsaro ta NSCDC sun yi nasarar kama wani sojan bogi mai shekaru 32 a Jihar Nasarawa.

The Punch ta rahoto cewa an kama wanda ake zargin, Moses Ayaka, a karamar hukumar Lafia, babban birnin jihar.

Sojan Bogi Mia Yaudara
Hotunan Wani Jami'in Sojan Bogi Da NSCDC Ta Kama a Nasarawa Yana Damfarar Mutane. Hoto: @MobilePunch/Collins Sunday.
Asali: Twitter

Kafin kama shi, wanda ake zargin, an ce ya dade yana damfarar mazauna garin.

Kara karanta wannan

Tashin hankali a kasar Muslunci yayin da mata suka fara kone Hijabi a wata zanga-zanga

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ayaka da kansa ya bayyana cewa ya damfari fiye da mutane 22 ya kwace musu kudi da ya kai N440,000.

Sojan Bogi
Hotunan Wani Jami'in Sojan Bogi Da NSCDC Ta Kama a Nasarawa Yana Damfarar Mutane. @MobilePunch/Collins Sunday.
Asali: Twitter

Rundunar ta ce za a mika shi hannun yan sanda domin zurfafa bincike da kuma gurfanar da shi a gaba kotu ya girbi abin da ya shuka.

Kano: Saboda Budurwa, Asirin Wani Da Sojan Bogi Ya Tonu, An Kama Shi Da Bindiga Da Harsashi

A wani rahoto mai kama da wannan, An kama wani mutum da ake zargi, da ba a riga an bayyana sunansa ba a Kano dauke da bindiga da albursai da kayan sojoji a Kano, Daily Trust ta rahoto.

An gano cewa wanda ake zargin yana basaja ne a matsayin soja, da suna M.A. Ibrahim, kuma yana kwatar kudade hannun mutane kan hanyar BUK road a jihar.

Kara karanta wannan

Alkawarin Aure: An Fara Gabatar da Shaidu Kan Hadiza Gabon a Kotun Shari'ar Musulunci

Shaidan gani da ido wanda ya nemi a boye sunansa ya ce wanda ake zargin yana zama ne a unguwar Danbare kusa da BUK, kuma ya rika fada wa mutane cewa shi kyafin ne a rundunar sojojin Najeriya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel